< 1 Chronicles 18 >

1 And after this Dauid smote the Philistims, and subdued them, and tooke Gath, and the villages thereof out of the hand of the Philistims.
Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
2 And he smote Moab, and the Moabites became Dauids seruants, and brought giftes.
Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
3 And Dauid smote Hadarezer King of Zobah vnto Hamath, as he went to stablish his border by the riuer Perath.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
4 And Dauid tooke from him a thousand charets, and seuen thousand horsemen, and twentie thousand footemen, and destroyed all the charets, but he reserued of them an hundreth charets.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
5 Then came the Aramites of Damascus to succour Hadarezer King of Zobah, but Dauid slewe of the Aramites two and twentie thousand.
Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
6 And Dauid put a garison in Aram of Damascus, and the Aramites became Dauids seruants, and brought giftes: and the Lord preserued Dauid wheresoeuer he went.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
7 And Dauid tooke the shieldes of gold that were of the seruants of Hadarezer, and brought them to Ierusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
8 And from Tibhath, and from Chun (cities of Hadarezer) brought Dauid exceeding much brasse, wherewith Salomon made the brasen Sea, and the pillars and the vessels of brasse.
Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
9 Then Tou King of Hamath heard howe Dauid had smitten all the hoste of Hadarezer King of Zobah:
Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
10 Therefore he sent Hadoram his sonne to King Dauid, to salute him, and to reioyce with him, because he had fought against Hadarezer, and beaten him (for Tou had warre with Hadarezer) who brought all vessels of golde and siluer and brasse.
sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
11 And King Dauid did dedicate them vnto the Lord, with the siluer and golde that hee brought from all the nations, from Edom, and from Moab, and from the children of Ammon, and from the Philistims, and from Amalek.
Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
12 And Abishai the sonne of Zeruiah smote of Edom in the salt valley eighteene thousand,
Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
13 And he put a garison in Edom, and all the Edomites became Dauids seruantes: and the Lord preserued Dauid wheresoeuer he went.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
14 So Dauid reigned ouer all Israel, and executed iudgement and iustice to all his people.
Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
15 And Ioab the sonne of Zeruiah was ouer the hoste, and Iehoshaphat the sonne of Ahilud recorder,
Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
16 And Zadok the sonne of Ahitub, and Abimelech the sonne of Abiathar were the Priests, and Shausha the Scribe,
Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
17 And Benaiah the sonne of Iehoiada was ouer the Cherethites and the Pelethites: and the sonnes of Dauid were chiefe about the King.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.

< 1 Chronicles 18 >