< Romans 8 >

1 So there is now no condemnation for those who are in Christ Jesus.
Saboda haka babu kayarwa yanzu ga wadanda ke cikin Almasihu Yesu.
2 The law of the Spirit of life in Christ Jesus has set me free from the law of sin and death.
Domin ka'idar ruhun rai a cikin Almasihu Yesu ta maishe mu 'yanttatu daga ka'idar zunubi da mutuwa.
3 What the law couldn't do because it was powerless due to our sinful nature, God was able to do! By sending his own Son in human form, God dealt with the whole problem of sin and destroyed sin's power in our sinful human nature.
Saboda abin da shari'a bata iya aikatawa ba domin kasawa ta wurin jiki, Allah ya yi. Ya aiko da dansa a kamanin jiki mai zunubi domin ya zama hadaya domin zunubi, sai ya yi Allah wadai da zunubi a cikin jiki.
4 In this way we could fulfill the good requirements of the law by following the Spirit and not our sinful nature.
Ya yi haka domin bukatar shari'a ta sami cika a cikinmu, mu da muke tafe ba ta gwargwadon jiki ba, amma ta gwargwadon ruhaniya.
5 Those who follow their sinful nature are preoccupied with sinful things, but those who follow the Spirit concentrate on spiritual things.
Wadanda ke rayuwa gwargwadon jiki sukan lura da al'amuran jiki, amma su da ke rayuwa a gwargwadon Ruhu sukan mai da hankali ga al'amuran Ruhu.
6 The sinful human mind results in death, but having the mind led by the Spirit results in life and peace.
To kwallafa rai ga jiki mutuwa ce, amma kwallafa rai ga Ruhu rai ne da salama.
7 The sinful human mind is hostile to God because it refuses to obey the law of God—in fact it never can,
Haka yake domin kwallafa rai ga jiki gaba yake da Allah, gama baya biyyaya ga shari'ar Allah, balle ma ya iya.
8 and those who follow their sinful nature can never please God.
Wadanda ke a jiki ba su iya faranta wa Allah zuciya.
9 But you're not following your sinful nature, but the Spirit—if it's true that the Spirit of God is living in you. For those that don't have the Spirit of Christ in them don't belong to him.
Duk da haka, ba ku cikin jiki amma a cikin Ruhu, idan gaskiya ne, Ruhun Allah na rayuwa cikinku. Amma idan wani ba shi da Ruhun Almasihu, shi ba na sa bane.
10 However, if Christ is in you, even though your body is going to die because of sin, the Spirit gives you life because you're now right with God.
In Almasihu na cikinka, jikin ka fa matacce ne ga zunubi, amma ruhu na rayuwa bisa ga adalci.
11 The Spirit of him who raised Jesus from the dead lives in you. He who raised Jesus from the dead will also give life to your dead bodies through his Spirit that lives in you.
Idan Ruhun wanda ya tada Yesu daga matattu na raye a cikinku, to shi wanda ya tada Almasihu da ga matattu za ya bada rai ga jikinku masu matuwa ta wurin Ruhunsa, da ke rayuwa a cikin ku.
12 So brothers and sisters, we don't have to follow our sinful nature that operates according to our human desires.
To, 'yan' uwa, muna da hakki amma ba bisa jiki ba, da za mu yi rayuwa bisa ga dabi'ar jiki.
13 For if you live under the control of your sinful nature, you're going to die. But if you follow the way of the Spirit, putting to death the evil things you do, then you will live.
Gama idan kun yi rayuwa gwargwadon jiki, za ku mutu kenan, amma idan ta wurin Ruhu ku ka kashe ayyukan jiki, za ku rayu.
14 All those who are led by the Spirit of God are God's children.
Gama duk wadanda Ruhun Allah ke bishe su, su 'ya 'yan Allah ne.
15 You were not given a spirit to enslave and terrify you once more. No, what you received was the spirit that makes you children in God's family. Now we can shout out, “God is our Father!”
Gama ba ku karbi ruhun bauta da ke sa tsoro ba. Maimakon haka, kun karbi ruhun diyanci, ta wurinsa muke tadda murya muna kira, “Abba, Uba!”
16 The Spirit himself agrees with us that we're God's children.
kansa na bada shaida tare da namu ruhun cewa mu 'ya'yan Allah ne.
17 If we're his children, then we're his heirs. We are heirs of God, and heirs together with Christ. But if we want to share in his glory we must share in his sufferings.
Idan mu 'ya'ya ne, ai mu magada ne kenan, magadan Allah. Kuma mu magada ne tare da Almasihu, hakika idan mun sha wahala tare da shi za a kuma daukaka mu tare da shi.
18 Yet I'm convinced that what we suffer in the present is nothing compared to the future glory that will be revealed to us.
Gama na yi la'akari cewa wahalonin zamanin nan ba su isa a kwatanta su da daukakar da za'a bayyana mana ba.
19 All of creation is patiently waiting, longing for God to reveal his children.
Saboda yadda halitta ke marmarin bayyanuwar 'ya'yan Allah.
20 For God allowed the purpose of creation to be frustrated.
Gama an kaskantar da halitta ga banza, ba da nufin ta ba, amma na shi wanda ya kaskantar da ita. Ta na cikin tabbacin alkawarin.
21 But creation itself waits in hope for the time when it will be set free from the slavery of decay and share the glorious freedom of God's children.
Cewa halitta kanta za ta kubuta daga bautar rubewa, kuma za a kawo ta zuwa ga 'yantarwa na yabon daukakar 'ya'yan Allah.
22 We know that all creation groans with longing, suffering birth-pains even up till now.
Gama mun sani dukan halitta na nishi da zafin nakuda tare har ya zuwa yanzu.
23 Not only creation, but we too, who have a foretaste of the Spirit, we groan inwardly as we wait for God to “adopt” us—the redemption of our bodies.
Ba haka kadai ba, amma ko mu kanmu, da ke nunar farko na Ruhu—mu kanmu muna nishi acikin mu, muna jiran diyancinmu, wato ceton jikinmu kenan.
24 For we were saved by hope. Yet hope that's already seen isn't hope at all. Who hopes for what they can already see?
Gama ta wanan hakikancewa aka cece mu. Amma dai abin da muke da tabbacin zai faru ba mu gan shi ba tukuna, domin wanene wa ke begen tabbatacce abin da yake gani?
25 Since we're hoping for what we haven't yet seen, we wait for it patiently.
Amma idan muna da tabbacin abin da ba mu gani ba tukuna, to sai mu jjira shi da hakuri.
26 Similarly the Spirit helps us in our weakness. We don't know how to speak with God, but the Spirit himself intercedes with and through us by groans that can't be put into words.
Hakanan, Ruhu kuma ke taimako a kasawarmu. Gama ba mu da san yadda zamu yi addu'a ba, amma Ruhu kansa na roko a madadinmu da nishe-nishen da ba'a iya ambatawa.
27 The one who examines the minds of everyone knows the Spirit's motives, because the Spirit pleads God's cause on behalf of the believers.
Shi da ke bidar zuciya yana sane da tunanin Ruhu, domin yana roko a madadin masu badagaskiya ta wurin nufin Allah.
28 We know that in all things God works for the good of those who love him, those who he has called to be part of his plan.
Mun san cewa ga wadanda ke kaunar Allah, yakan aikata dukan al'amura domin su zuwa ga alheri, ga duk wadanda aka kira bisa ga nufinsa. Dukan abubuwa sukan zama alheri.
29 For God, choosing them in advance, set them apart to be like his Son, so that the Son would be the first of many brothers and sisters.
Saboda wadanda ya sani tuntuni su ne ya kardara su zama da kamanin dansa, domin ya zama dan fari a cikin 'yan'uwa masu yawa.
30 Those that he chose, he also called; and those that he called, he also made right; and those that he made right, he also glorified.
Su da ya kaddara, ya kiraye su. Wadanda ya kira, su ya kubutar. Su da ya kubutar, sune kuma ya daukaka.
31 So what's our response to all this? If God is for us, who can be against us?
Me zamu ce game da wadannan al'amura? Idan Allah na tare da mu, wake gaba da mu?
32 God, who did not hold back his own Son, but gave him up for all of us, won't he also freely give us everything?
Shi da baya hana dansa ba, amma ya bada shi a madadinmu dukka, me zai hana shi bamu dukkan abubuwa a yalwace tare da shi?
33 Who can accuse God's special people of anything? It's God who sets us right,
Wa zaya kawo wata tuhuma ga zababbu na Allah? Allah ne ke “yantarwa.
34 so who can condemn us? It's Christ Jesus who died—more importantly, who was raised from the dead—who stands at God's right-hand, presenting our case.
Wanene ke hukumtawa? Almasihu ne da ya mutu sabili da mu har ma fiye da haka, shi wanda kuma aka tasar. Yana mulki tare da Allah a wuri mai daukaka, shi ne kuma ya ke roko sabili da mu.
35 Who can separate us from Christ's love? Can oppression, distress, or persecution? Or hunger, poverty, danger, or violence?
Wa za ya raba mu da kaunar Allah? Kunci, ko bacin rai, ko tsanani, ko yunwa, ko tsiraci, ko hadari, ko takobi?
36 Just as Scripture says, “For your sake we're in danger of being killed all the time. We're treated like sheep to be slaughtered.”
Kamar yadda aka rubuta, “Saboda kai ake kisanmu dukkan yini. An mai da mu kamar tumaki yanka.”
37 No—in all that happens to us we're more than conquerors through him who loved us.
A dukan al'amuran nan mun fi karfi a ce da mu masu nasara ta wurin shi da ke kaunar mu.
38 I'm absolutely convinced that neither death nor life, neither angels nor devils, neither the present nor the future, nor powers,
Gama na tabata cewa ko mutuwa, ko rai, ko mala'iku, ko mulkoki, ko al'amuran yanzu, ko al'amura masu zuwa, ko iko,
39 neither height nor depth, in fact nothing in all creation can separate us from the love of God in Christ Jesus our Lord.
ko tsawo, ko zurfi, kai ko wace irin halitta, ba su isa su raba mu da kaunar Allah, da ke a cikin Almasihu Yesu Ubangijin mu ba.

< Romans 8 >