< Revelation 6 >
1 I watched as the Lamb broke open the first of the seven seals. I heard one of the four living creatures shout with a thunderous voice, “Come!”
Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, ''Zo!”
2 I looked and saw a white horse. Its rider was holding a bow. He was given a crown, and he rode out conquering so that he would be victorious.
Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.
3 When he opened the second seal, I heard the second living creature say, “Come!”
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, ''Zo!''
4 Another horse came out, a red one. Its rider was given a large sword, and the power to take away peace from the earth so that people would slaughter one other.
Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.
5 When he opened the third seal, I heard the third living creature say, “Come!” I looked and saw a black horse. Its rider was holding a pair of scales in his hand.
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, ''Zo!'' Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa.
6 I heard what seemed to be a voice coming from among the four living creatures that said, “Two pounds of wheat cost a day's wages, and three pounds of barley cost the same. But don't damage the oil or the wine.”
Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, “Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi.”
7 When he opened the fourth seal, I heard the fourth living creature say, “Come!”
Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, ''Zo!''
8 I looked and saw a pale horse. The rider was called Death, and Hades followed him. They received authority over a quarter of the earth to kill people by the sword, by famine, by plague, and by wild beasts. (Hadēs )
Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya. (Hadēs )
9 When he opened the fifth seal, I saw underneath the altar those who had been killed because of their dedication to the word of God and their faithful witness.
Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike.
10 They cried out, shouting, “How long, Lord who is holy and true, before you will judge and bring to justice those on earth who spilled our blood?”
Suka yi kuka da babban murya, ''Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu?
11 Each one of them was given a white robe, and they were told to wait for a little longer until their number was complete—their fellow-believers and brothers who would be killed like them.
Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.
12 When he opened the sixth seal there was a tremendous earthquake. The sun turned black like hair sackcloth and the whole moon turned red like blood.
Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini.
13 The stars of heaven fell to earth like unripe figs falling from a fig tree shaken by a windstorm.
Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada.
14 The sky disappeared like a scroll rolling up, and all the mountains and islands were moved from where they were.
Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.
15 The kings of the earth, the great leaders, the wealthy, the powerful, and all people, slave or free, hid themselves in caves and among the rocks in the mountains.
Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka.
16 They called on the mountains and the rocks, telling them, “Fall upon us! Hide us from the face of the one who sits on the throne, and from the judgment of the Lamb.
Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, “Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon.
17 For the terrible day of their judgment has come, and who can stand against it?”
Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?''