< Revelation 2 >

1 “Write this to the angel of the Ephesus church: This is what the one who holds the seven stars in his right hand says, the one who walks among the seven golden candlesticks:
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.
2 I know what you've accomplished, your hard work and perseverance. I know you can't tolerate evil people, and how you investigated those who claimed to be apostles but are not, and discovered they were frauds.
Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne.
3 I know about your patience, and what you endured for my sake—and that you didn't give up!
Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.
4 But I have something against you: you have neglected your first love.
Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko.
5 So remember how far you've fallen—repent and go back to what you were doing at first. Otherwise I'll come to you and I will remove your candlestick from where it is—unless you repent.
Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake.
6 However, you do have this to your credit: you hate the actions of the Nicolaitans, just as I do.
Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.
7 If you have ears, listen to what the Spirit is telling the churches. I will give to those who are victorious the privilege of eating from the tree of life, which stands in the Paradise of God.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.
8 Write this to the angel of the Smyrna church: This is what the first and last says, the one who was dead and came back to life:
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.
9 I know the troubles you are going through, and how poor you are (but you are rich), and the abuse from those who say they are Jews but are not, but belong to Satan's synagogue.
Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne.
10 Don't be afraid about what you are going to suffer. Yes, the devil will throw some of you into prison to test you, and you will suffer persecution for ten days. Just remain faithful, even if it means death, and I will give you the crown of life!
Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
11 If you have ears, listen to what the Spirit is telling the churches. The second death will not harm those who are victorious.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.
12 Write this to the angel of the Pergamum church: This is what the one holding the sharp two-edged sword says:
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.
13 I know you're living where Satan has his throne, and that you have stayed true to me. You have not denied your trust in me, even when my faithful witness Antipas was killed right among you there where Satan lives!
Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.
14 But I have a few things against you: There are some among you who hold to the teaching of Balaam, who taught Balak how to entrap the children of Israel by means of eating food sacrificed to idols and committing sexual sins.
Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci.
15 Similarly you also have some who hold to the teaching of the Nicolaitans.
Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa.
16 So repent, or soon I will come to you and fight against them using the sword of my mouth.
Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.
17 If you have ears, listen to what the Spirit is telling the churches. I will give the hidden manna to those who are victorious. I will give them a white stone with a new name written on it that nobody knows except those who receive it.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.
18 Write this to the angel of the Thyatira church: This is what the Son of God says, the one who has eyes like flaming fire and feet like polished brass.
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.
19 I know what you have accomplished, your love and faithfulness and service and perseverance, and that you are doing more now than when you first believed.
Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.
20 But I have something against you: you are allowing the woman called Jezebel who calls herself a prophetess to teach my followers, leading them astray into sexual sins, and to eat food sacrificed to idols.
Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka.
21 I gave her time to repent of her sexual sins, but she's not willing to repent.
Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya.
22 So I'm throwing her into a bed together with her adulterous partners and they will suffer terribly unless they repent of what they have done with her.
Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta.
23 I will put her children to death. Then all the churches will know that I am the one who examines thoughts and motives. I will repay each of you according to what you've done.
Zan kashe’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.
24 For the rest of you there in Thyatira who don't follow this teaching, who have not learned Satan's ‘deep depravities’ as they are called, I don't place on you any other burden. I say to you,
Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba.
25 ‘Just hold on to what you have until I come.’
Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
26 I will give authority over the nations to those who are victorious and who do what I say until the end.
Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
27 He will rule the nations with an iron rod, breaking them into pieces like clay pots. In the same way that I received authority from my Father,
‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
28 I will give them the morning star.
Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
29 If you have ears, listen to what the Spirit is telling the churches.”
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.

< Revelation 2 >