< Revelation 13 >
1 And the dragon stood on the sea shore. Then I saw a beast rising out of the sea. He had ten horns and seven heads, with ten small crowns on his horns, and had blasphemous names on his heads.
Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku. Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo.
2 The beast I saw looked like a leopard, but his feet looked like those of a bear, and his mouth looked like that of a lion. The dragon gave the beast his power, his throne, and great authority.
Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.
3 One of his heads seemed to have suffered a death-blow, but this fatal wound had been healed. The whole world was filled with wonder at the beast,
Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban.
4 and they worshiped the dragon because he had given his authority to the beast; and they worshiped the beast, asking “Who is like the beast? Who could defeat him?”
Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, “Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?”
5 He was given the ability to make great boasts and speak blasphemies, and he was also given the authority to do this for forty-two months.
Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu.
6 As soon as he opened his mouth he spoke blasphemies against God, insulting his character, his sanctuary, and those who live in heaven.
Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.
7 The beast was given power to attack believers and defeat them, and he was also given authority over every people, tribe, language, and nation.
Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma.
8 Everybody living on earth will worship him, those whose names had not been written in the book of life—the book of life that belongs to the Lamb slain from the beginning of the world.
Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.
9 If you have ears, listen!
Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi.
10 Anyone who has to go into captivity will go into captivity; anyone who has to die by the sword will die by the sword. This demonstrates the patient endurance and confidence in God of the believers.
Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.
11 Then I saw another beast, rising up from the earth. He had two horns like a lamb, but he spoke like a dragon.
Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji.
12 He imposed the same authority as the first beast on his behalf, and made the earth and those who live there worship the first beast, whose fatal wound had been healed.
Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.
13 He performed great miracles, even bringing fire down from heaven to earth while people watched.
Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane.
14 He deceived those who live on the earth by the miracles he performed on behalf of the beast, ordering the people that they should make an image for the beast who had received the fatal sword wound but came back to life.
Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.
15 He was permitted to breathe life into the image of the beast so that it could speak, ordering anyone who did not worship it put to death.
Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban.
16 He made everyone, whether weak or powerful, rich or poor, free or slave, receive a mark on their right hand or on their foreheads.
Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi.
17 Nobody was permitted to buy or sell except those who had the mark, which was the name of the beast or the number of his name.
Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.
18 Wisdom is needed here. Whoever has understanding should calculate the number of the beast, for it is the number of a man. His number is 666.
Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.