< Psalms 83 >
1 A song. A psalm of Asaph. God, please do not stay silent! You can't remain unmoved! God, you must not keep quiet!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Can't you hear the roars of your enemies? Can't you see how those who hate you are defiantly lifting up their heads?
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 They invent cunning plans to conspire against your people; they plot against those you treasure.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 They say, “Come on! Let's destroy them as a nation so the name ‘Israel’ will be completely forgotten.”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 They all agree in their conspiracy; they've made a treaty together to attack you—
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 the people of Edom, the Ishmaelites, Moab, and the Hagirites;
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 the people of Gebal and Ammon and Amalek, Philistia, and the inhabitants of Tyre.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Assyria too has joined them, allied with the descendants of Lot. (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do to them what you did to Midian, what you did to Sisera and Jabin at the Kishon River.
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 They were destroyed at Endor and became like manure to fertilize the ground.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their leaders like Oreb and Zeeb; all their rulers like Zebah and Zalmunna,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 for they said, “Let's take the pastures of God for ourselves!”
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 My God, make them like whirling tumbleweeds, chaff blown away by the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Just like fire that burns the forest, a flame that sets fire to the mountains,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 in the same way chase them down with your storm, terrify them with your whirlwind.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Shame them in defeat so that they come to you, Lord!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Make them ashamed, terrify them forever so that they die in disgrace.
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Let them understand that you alone, called the Lord, are the Most High who rules over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.