< Psalms 81 >
1 For the music director. On the gittith. A psalm of Asaph. Sing aloud to God our strength; shout for joy to the God of Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Start the song! Play the tambourine, sweet-sounding lyre, and harp.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Blow the trumpet at the new moon, and at full moon, to begin our festivals,
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 for this is a rule for Israel, a regulation of the God of Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 God made this statute for Joseph when he opposed the land of Egypt. I heard a voice I didn't know, saying:
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 “I took the load from your shoulders; I freed your hands from carrying heavy baskets.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 In your suffering you cried out to me, and I saved you. I answered you from the thundercloud. I tested you at the waters of Meribah. (Selah)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 My people, listen to my warnings! Israel, please listen to me!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 There must not be a strange god among you; you must never bow down to foreign gods and worship them.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 I am the Lord your God who brought you out of the land of Egypt. Open your mouth wide and I will fill it.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 But my people didn't listen to me. Israel didn't want anything to do with me.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 So I sent them away to follow their stubborn thinking, living as they chose.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 If only my people would listen to me; if only Israel would follow my ways!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 It wouldn't take me long to conquer their enemies, to strike down their foes.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Those who hate the Lord would cringe before him, forever doomed.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 But I would feed you the best wheat and satisfy you with honey from the rock.”
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”