< Psalms 79 >

1 A psalm of Asaph. God, heathen nations have invaded your land. They have defiled your holy Temple. They have turned Jerusalem into heaps of rubble.
Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
2 They have given the dead bodies of your servants as food to the birds of the air, the flesh of your faithful people to the beasts of the earth.
Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
3 They have poured out the blood of Jerusalem's people like water all through the city; no one remains to bury the dead.
Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
4 We have been made a mockery before our neighbors, ridiculed and laughed at by those around us.
Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
5 How long, Lord? Will you be angry with us forever? Will your jealousy always burn like fire?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
6 Pour out your anger on the heathen nations that don't know you, and on those kingdoms that don't worship you!
Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
7 For they have destroyed the descendants of Jacob, and turned our country into a wasteland.
gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
8 Don't hold the sins of our forefathers against us! Come to us quickly for we desperately need your compassion.
Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
9 Help us, God of our salvation, because of your wonderful character! Save us and forgive us our sins because that's the kind of person you are!
Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
10 Why should the heathen nations be able to say, “Where is their God?” May they experience your punishment for shedding the blood of your servants, and may we see it.
Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
11 Listen to the groans of the prisoners; with your great power save those condemned to die.
Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
12 Pay each of these neighbors back seven times for the scorn and ridicule they directed against you, Lord.
Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
13 Then we your people, the flock of your pasture, will praise you forever. We will thank you for all generations to come.
Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.

< Psalms 79 >