< Psalms 77 >
1 For Jeduthun, the music director. A psalm of Asaph. I cry out to God for help—I even shout. If only he would listen to me!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 When I was in trouble I prayed to the Lord. All night long I stretched out my hands to him in prayer but nothing brought me any comfort.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I thought about God, groaning loudly; I meditated on him, but I was discouraged. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 You stop me going to sleep; I'm so upset I can't even talk.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I think of the old days, years ago.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 I remember the songs I sung in the night. I meditate and ask myself:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Has the Lord given up on me forever? Won't he ever be pleased with me again?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Has his trustworthy love disappeared forever? Have his promises permanently ended?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Has God forgotten to be kind? Has he angrily slammed the door shut on his compassion? (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Then I said, “This is what hurts me the most: the Most High doesn't treat me the way he used to.”
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I remember what you have done, Lord; I remember all the wonderful things you did long ago.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 I will think about all you have accomplished; I will think deeply about how you have acted.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 God, your ways are holy; is any god as great as you?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 You are the God who does wonderful things! You have revealed your power to the nations.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Through your strength you saved your people, the descendants of Jacob and Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 When the waters saw you, God, when they looked they trembled! Yes, they shook down to the very depths!
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 The clouds poured rain down; the skies crashed with thunder; your lightning flew like arrows.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 Your thunder rumbled from the whirlwind; lightning flashes lit up the world; the earth quaked and shook.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Your way led through the sea; your path passed through the deep sea; yet your footprints were invisible.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 You led your people like a flock, shepherded by Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.