< Psalms 58 >

1 For the music director. According to “Do Not Destroy.” A psalm (miktam) of David. You leaders, do you really say what is right? Do you judge people fairly?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 No, for in your minds you plan evil. You cause violence everywhere!
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 The wicked are sinners from birth; from the moment they're born they tell lies.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 They have venom like that of a poisonous snake, and just like a cobra they stop listening,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 refusing to hear the voice of the snake charmers or the spellbinders.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 God, break their teeth, and smash the jaws of these lions, Lord.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 May they vanish like water that flows away; when they shoot their arrows may they miss their mark.
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 May they be like the slime of snails that dissolves away, like a stillborn child that never saw the light of day.
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Before the cooking pot is hot from burning thorns, whether fresh or dry, God will blow them away.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Those who live right will be happy when they see there is punishment; they will wash their feet in the blood of the wicked.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 They will say, “There is definitely a reward for those who live right; there is certainly a God who judges fairly on earth.”
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< Psalms 58 >