< Psalms 55 >

1 For the music director. With stringed instruments. A psalm (maskil) of David. God, please hear my prayer; don't ignore my cry for help!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Please listen, and give me an answer. I'm terribly troubled by my problems! I'm frantic!
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 For my enemies are screaming at me; the wicked are intimidating me. They rain down suffering on me, angrily assaulting me in their hatred.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 My heart thumps in agony! Terrified, I feel I'm about to die!
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 I'm in a panic, trembling with fear; feelings of horror wash over me.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 I tell myself, If only God would give me wings like a dove so I could fly away and be at peace!
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 I would fly far away to escape, and stay in the wilderness. (Selah)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I would hurry to a place to hide, out of the wind, safe from the raging storm.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Confuse them, Lord! Muddle what they're saying, for I see violence and conflict in the city.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 They patrol the city walls day and night, and wickedness and trouble are within the city.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 The ones causing destruction are inside the city; frauds and cheats are always on the streets.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 The problem is that it's not an enemy who mocks me—I could stand that. It's not someone who hates me who insults me—I could avoid them.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 No, it's you, a man just like me, my best friend who I know so well!
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 Our friendship was so close. We used to have great talks together as we walked with everyone to the house of God.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 May death come quickly to them; may they go down into the grave alive, because evil finds its home in them. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 As for me, I cry out to God, and the Lord will save me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 I weep and groan morning, noon, and night, and he listens to me.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 He rescues me, keeping me safe and sound from my attackers, because there are so many against me.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God who has ruled from the beginning will hear me and answer them. (Selah) For they refuse to change and don't respect God.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 As for my best friend, he attacked his friends who had no quarrel with him; he broke the promises he had made to them.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 What he says is as smooth as butter, but inside he plans war; his words are as soothing as oil, but they cut like sharp swords.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Throw your burdens onto the Lord and he will take care of you. He will never allow those who live right to fall.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 But you, God, will bring down murderers and liars, throwing them into the pit of destruction before they have even lived half their lives. As for me, I will trust in you.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >