< Psalms 44 >
1 For the music director. A psalm (maskil) of the sons of Korah. God, we have heard with our own ears—our forefathers have told us—all you did in their times, long ago.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Through your power you drove out the other nations so you could settle our ancestors there; you defeated the nations and you sent our ancestors to occupy the land.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 They did not conquer the land using their swords; it was not through their own strength that the victory was won—it was by your strength, your power, and your presence with them, because you loved them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 God, you are my King; command victories for Jacob!
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Only through you can we repel our enemies; only in your name can we defeat our opponents.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 I do not trust my bow; I do not have confidence in my sword to save me.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 You are the one who saves us from our enemies; you defeat those who hate us.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 God, we proudly thank you all day long, and praise your name forever. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 But now you have rejected and disgraced us; you no longer accompany our armies.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 You made us run from our enemies, and those who hate us have taken whatever they wanted.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You have handed us over like sheep to be slaughtered; you have scattered us among the other nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 You have sold your own people for next to nothing, making no profit on the sale.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 You have made a mockery of us before our neighbors, we are ridiculed and laughed at by those around us.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 You have made us a joke to the other nations; they scornfully shake their heads at us.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 We are humiliated all day long; we hold our heads in shame,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 because of all the insults from the people mocking us, because our vengeful enemies are right in front of us.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this has happened to us even though we didn't forget you; we haven't been unfaithful to the promises we made to you.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 We have not turned away from you, not in thought, nor in action.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Even so, you crushed us, and made us into a jackal's den. You have covered us with the darkness of death.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we had forgotten the name of our God, or worshiped other gods,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 wouldn't God have been aware of this, because he knows everyone's thoughts?
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 But because of you we are killed all day long; we're considered just sheep to be slaughtered.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Lord, wake up! Why are you sleeping? Get up! Don't turn your back on us forever!
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why do you look away from us and take no notice of our suffering and misery?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 We lie ruined in the dust, our bodies face down in the dirt.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Stand up! Come and help us! Save us because of your trustworthy love!
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.