< Psalms 21 >
1 For the music director. A psalm of David. The king celebrates your strength, Lord; he is so happy you made him victorious!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 You gave him everything he wanted; you didn't hold anything back he asked for.
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 You welcomed him on his return with special blessings; you placed a crown of pure gold on his head.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 He asked you to give him a good life, and you gave him a long life, forever and ever.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Your victories brought him great glory; you granted him splendor and majesty.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 You give him blessings forever. He is full of joy because you are with him.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 For the king trusts in the Lord; he stands firm because of the trustworthy love of the Most High.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 You, the king, will find and capture all your enemies; you will seize everyone who hates you.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 When you appear on the scene you will burn them up like in a furnace; the Lord in his anger will destroy them, burning them up with fire.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 You will wipe out their children from the earth, their descendants from humankind.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Though they plot evil against you, their malicious schemes will not succeed.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 They will turn and run away when they see your arrows fired at them.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Rise up, Lord, for you are strong! We will sing and praise your power!
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.