< Psalms 147 >
1 Praise the Lord, for it's good to sing praises to our God! Praise is wonderful and beautiful!
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 The Lord is rebuilding Jerusalem, gathering together the people of Israel who have been scattered.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 He heals the broken-hearted, and bandages the wounded.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 He knows how many stars he made, and commands all of them by name.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Our Lord is great! His power is immense! There's no limit to what he understands!
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 The Lord helps those who are bowed down to get up; but he grinds the wicked into the ground.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Sing thanks to the Lord! Sing praises to our God with a harp!
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 He covers the sky with clouds to bring rain to the earth, and makes the grass grow on the hills.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 He gives food to the animals, and to the baby ravens when they call.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 The Lord doesn't appreciate the strength of war-horses or value human power.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 What the Lord values are those who follow him, those who put their confidence in his trustworthy love.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Jerusalem, praise the Lord! Zion, praise your God!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 He makes the bars on your city gates strong, and blesses your children around you.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 He keeps the borders of your land safe from attack; he provides you with plenty of the finest wheat.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 He sends his commands around the world—they're quickly implemented.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 He sends snow as white as wool, and scatters frost like ashes.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 He throws hail like stones. Who can stand the cold he sends?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Then he sends out his command and it melts; he blows on it and the water flows.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 He proclaims his word to Jacob; his rules and laws to Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He has not done this for any other nation—they don't know his laws. Praise the Lord!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.