< Psalms 129 >

1 A song for pilgrims going up to Jerusalem. Many enemies have attacked from the time I was young. Let everyone in Israel say:
Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
2 Many enemies have attacked from the time I was young, but they never defeated me.
sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
3 They beat me on my back, leaving long furrows as if it had been ploughed by a farmer.
Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
4 But the Lord does what is right: he has cut me free from the ropes of the wicked.
Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
5 May everyone who hates Zion be driven back in humiliating defeat.
Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
6 May they be like grass that grows on a roof that withers before it can be harvested,
Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
7 There's not enough even for a reaper to hold, not enough even for the binder to bind.
da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
8 May passers-by not say to them, “The blessing of the Lord be on you; we bless you in the name of the Lord.”
Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”

< Psalms 129 >