< Psalms 112 >

1 Praise the Lord! Happy are those who respect the Lord, who love to do what he says!
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Their descendants will prosper in the land; the children of those who do good will be blessed.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Their families will be wealthy; the good they do has eternal results.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Light shines in the darkness for those who live right, for those who are gracious, compassionate, and good.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Good things come to those who are generous in their lending and are honest in doing business.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 They will never fall. Those who live right won't be forgotten.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 They aren't afraid of bad news because they rely totally on the Lord.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 They are confident and brave, and see their enemies defeated.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 They share generously, giving to the poor; the good they do has eternal results. They are greatly respected.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 The wicked observe all this and are mad; they gnash their teeth in anger. They waste away, and all that they hoped for comes to nothing.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Psalms 112 >