< Psalms 107 >

1 Thank the Lord, for he is good! His trustworthy love continues forever!
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let those the Lord has saved say that they are saved; those he has rescued from the power of the enemy.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 He has gathered them together from distant lands, from the east and the west, the north and the south.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 They wandered in the desert wilderness, unable to find a way to a city where they could live.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hungry and thirsty, they became very discouraged.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Then they cried out to the Lord to help them in their troubles, and he saved them from their suffering.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 He led them along a straight way to a city where they could live.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Let them praise the Lord for his trustworthy love, and for all the wonderful things he does for people.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 For he gives drink to those who are thirsty, and food to those who are hungry.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Some sat in complete darkness, prisoners of misery and bound with iron chains,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 for they had rebelled against what God had said; they had rejected the guidance of the Most High.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 So he humbled their pride with the troubles of life; they tripped over and no one was there to stop them falling.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Then they called out to the Lord for help in their troubles, and he saved them from their suffering.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 He brought them out of complete darkness, he broke their chains to pieces.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Let them praise the Lord for his trustworthy love, and for all the wonderful things he does for people.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 For he breaks down the bronze doors, and cuts through the iron bars.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 They were stupid because they rebelled; they suffered for their sins.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 They didn't want to eat; they were at death's door.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Then they called out to the Lord for help in their troubles, and he saved them from their suffering.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 He gave the command and he healed them; he saved them from the grave.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Let them praise the Lord for his trustworthy love, and for all the wonderful things he does for people.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Let them present thank offerings and sing with joy about what he has done.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Those who set sail in ships, crossing the seas to earn their living,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 they have seen the Lord's incredible power at work—the wonderful things he did in the deepest oceans.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 He only had to speak to cause a stormy wind that stirred up towering waves,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 lifting the ships high in the air and then plunging them down. The sailors were so terrified that their courage melted away.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 They staggered around, falling from side to side like drunks—all their seamanship skills were useless.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Then they cried out to the Lord to help them in their troubles, and he saved them from their suffering.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 He calmed the storm, the waves were quiet.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 The sailors were so happy when it all calmed down, and he brought them to the harbor they wanted.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Let them praise the Lord for his trustworthy love, and for all the wonderful things he does for people.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Let them say how wonderful he is in front of the whole congregation and the elders.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 He dries up rivers and turns the land into a desert; the water springs stop flowing and the earth turns dry and dusty.
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Fruitful ground becomes a salty wasteland because of the wickedness of those living there.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 But he also turns around and makes pools of water in the desert, and makes water springs flow in a dry and dusty land.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 He brings hungry people to live there—a place they can build their cities.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 They sow their fields and plant their vineyards, producing a good harvest.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 He takes care of them, and their numbers increase dramatically—their cattle too!
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 When they become few, brought low by oppression, misery, and sorrow,
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 He pours out his contempt on their leaders, making them wander, lost in the wilderness.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 But he lifts the poor out of their troubles, and makes their families as big as flocks.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Those who live right will observe what is happening and be glad, but the wicked will be silenced.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Those who are wise will pay attention to all this, and thoughtfully reflect on the Lord's trustworthy love.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalms 107 >