< Psalms 102 >
1 A prayer from someone who is suffering and is tired out, pouring out their troubles to the Lord. Lord please hear my prayer, my cry for help!
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Don't hide your face from me in my time of trouble! Turn and listen to me, and answer me quickly when I call.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 My life is disappearing like smoke; my body feels like it's on fire!
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 I'm like grass that's dried up, withered away—I even forget to eat!
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 All my groaning has worn me out; my bones show through my skin.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 I'm like a desert owl, like a little owl among the ruins.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 I can't sleep. I'm like a lonely bird on a rooftop.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 My enemies taunt me all day long. They mock me and swear at me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Ashes are the food I eat; my tears drip into my drink,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 because of your anger and hostility, for you have picked me up and tossed me away.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 My life is fading away like a shadow that lengthens—I'm withering away like grass.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 But you, Lord, reign forever, your fame will last for all generations.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 You will take action and have pity on Jerusalem, for it's time to be kind to the city, the time has come.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 For the people who follow you love its stones; they value even its dust!
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Then the nations will be in awe of who you are, Lord; all the kings of the earth will be in awe of your glory.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 For the Lord will rebuild Jerusalem; he will appear in glory.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 He will pay attention to the prayers of the homeless; he will not disregard their requests.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Let this be recorded for generations to come, so that people yet to be born may praise the Lord:
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 The Lord looked down from above, from the heights of his holy place; he looked down from heaven to the earth,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 to respond to the groans of prisoners, to set free the children of death.
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 As a result the wonderful nature of the Lord will be celebrated with praise in Jerusalem,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 when the people of many kingdoms gather together to worship the Lord.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 But as for me, he broke my health while I was still young, cutting my life short.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 I cried out, “My God, don't take my life while I'm young! You are the one who lives forever.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Long ago you created the earth; you made the heavens.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 They will come to an end, but you will not. They will all wear out, like clothes—you will change them, and throw them away.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 But you are the one who always is; your years never come to an end.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Our children will live with you, and our children's children will grow in your presence.”
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”