< Proverbs 8 >
1 Isn't wisdom calling? Isn't understanding raising her voice?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 On the top of the hill by the road, she stands up at the crossroads.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Beside the gates of the town, right there at the entrance, she cries out:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 “I'm calling out to you, everyone! My call is to everyone in the whole world!
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 If you're immature, learn how to grow up. If you're stupid, learn what makes good sense.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Listen to me because I have valuable things to explain to you.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 I say what's right, because I tell the truth and I hate wickedness in all its forms.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 All the words I say are true; none are false or misleading.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 My words are straightforward to anyone with understanding; they are correct to those who have knowledge.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Choose my instruction over silver; choose knowledge over pure gold.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 For wisdom is more valuable than rubies; everything you could ever want just doesn't compare!
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 I, wisdom, am at home with good decisions. I know how to find knowledge and discernment.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Honoring the Lord means hating evil. So I hate pride and arrogance, wicked behavior and telling lies.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 I have advice and good judgment; I know what makes sense, and I have power.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 It's because of me that kings reign, and rulers issue fair decrees.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 It's because of me that leaders and nobles govern—all who rule justly.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 I love those who love me, and those who really look for me will find me.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 With me go riches and honor, lasting wealth and prosperity.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 The fruit I produce is better than gold, even pure gold, and my harvest is better than even the best silver.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 I live in a way that's right; I follow the paths of justice.
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 I grant wealth to those who love me; I fill their treasure storehouses.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 The Lord created me first of all; I was made before anything else.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 I was formed a long time ago, at the first, before the world began.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 I was born when there were no ocean depths, when there were no springs pouring out water.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 I was born before the mountains or the hills had been formed,
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 when he hadn't made the earth and its fields or any of the earth's dust.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 I was there when he placed the heavens in position, when he drew the horizon over the ocean,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 when he made the clouds in the sky above, when he created the springs of the oceans,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 when he set limits on the sea so that the waters would not go farther than he ordered, and when he laid out the foundations of the earth.
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Then I was beside him as a master craftsman. I made him happy every day, and I was always full of joy in his presence.
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 I was so happy in the world he created, celebrating together with human beings.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 And now, my sons, listen to me, for happy are those who follow my ways.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Listen to my instruction and be wise—do not reject it.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Happy are those who listen to me, watching for me every day at my doors, waiting at my entrance way.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 For those who find me, find life, and are accepted by the Lord.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 But those who don't find me hurt themselves; everyone who hates me loves death.”
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”