< Numbers 24 >

1 When Balaam saw that the Lord wanted to bless Israel, he chose not to use divination as he had previously. Instead he turned towards the desert,
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 and as he looked at Israel camped there according to their respective tribes, the Spirit of God came on him.
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 He gave a declaration, saying:
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 “This is the prophecy of Balaam, son of Beor, the prophecy of a man who sees with eyes are wide open, the prophecy of one who hears the words of God, who sees the vision given by Almighty, who bows down in respect with open eyes.
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 How well set out your tents are, Jacob; the places where you live, Israel!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 They look like wooded valleys, like gardens beside a river, like aloe trees the Lord has planted, like cedars at the water's edge.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 The Israelites will pour out bucketfuls of water; their descendants will have plenty of water. Their king will be greater than King Agag; their kingdom will be glorious.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 God led them out of Egypt with great power, as strong as an ox, destroying enemy nations, breaking their bones, piercing them with arrows.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 They are like a lion that crouches and lies down. They are like a lioness that nobody dares to disturb. Those who bless you will be blessed; those who curse you will be cursed.”
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 Balak got angry with Balaam, and beat his fists together. He told Balaam, “I brought you here to curse my enemies, and now look! You keep on blessing them, doing it three times.
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 Leave right now! Go home! I promised to pay you well, but the Lord has made sure you wouldn't receive any payment.”
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 But Balaam said to Balak, “Didn't I already explain to the messengers you sent
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 that even if you gave me your whole palace full of silver and gold, I couldn't do anything I wanted or disobey the command of the Lord my God in any way? I can only say what the Lord tells me.
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 Listen! I'm going back home now to my own people, but first let me warn you what these Israelites are going to do to your people in the future.”
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 Then Balaam gave a declaration, saying, “This is the prophecy of Balaam, son of Beor, the prophecy of a man whose eyes are wide open
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 the prophecy of one who hears the words of God, who receives knowledge from the Most High, who sees the vision given by Almighty, who bows down in respect with open eyes.
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 I see him, but this isn't now. I observe him, but this isn't close at hand. In the future a leader like a star will come from Jacob, a ruler with a scepter will come to power from Israel. He will crush the heads of the Moabites, and destroy all the people of Seth.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 The country of Edom will be conquered, his enemy Seir will be conquered, and the Israelites will be victorious.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 A ruler from Jacob will come and destroy those left in the city.”
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 Balaam turned his attention to the Amalekites and gave this declaration about them, saying, “Amalek was first among the nations, but they will end up being destroyed.”
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 He turned his attention to the Kenites and gave this declaration about them, saying, “Where you live is safe and secure, like a nest on a cliff-face.
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 But Kain will be burned down when Assyria conquers you.”
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 Then Balaam gave another declaration, saying, “It's a tragedy! Who can survive when God does this?
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 Ships will be sent from Cyprus to attack Assyria and Eber, but they too will be permanently destroyed.”
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 Then Balaam left and returned to his own country, and Balak left too.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Numbers 24 >