< Numbers 13 >
2 “Send some men to explore the land of Canaan, the country I'm giving to the Israelites. Choose one of the leaders from each of the tribes to go and do this.”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 Moses did as the Lord had ordered and sent the men out from the Desert of Paran. They were all leaders of the Israelites.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 Their names were: Shammua son of Zaccur, from the tribe of Reuben.
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 Shaphat, son of Hori, from the tribe of Simeon.
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 Caleb, son of Jephunneh, from the tribe of Judah.
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 Igal, son of Joseph, from the tribe of Issachar.
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 Hoshea, son of Nun, from the tribe of Ephraim.
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 Palti son of Raphu, from the tribe of Benjamin.
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 Gaddiel, son of Sodi, from the tribe of Zebulun.
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 Gaddi, son of Susi, from the tribe of Manasseh (a tribe of Joseph).
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 Ammiel, son of Gemalli, from the tribe of Dan.
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 Sethur, son of Michael, from the tribe of Asher.
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 Nahbi, son of Vophsi, from the tribe of Naphtali.
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 Geuel, son of Machi, from the tribe of Gad.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 These were the names of the men that Moses sent to explore the country. Moses called Hoshea Joshua.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Moses sent them out to explore the land of Canaan, telling them, “Go through the Negev and on into the hill country.
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 See what the place looks like, and find out about the people living there—are they strong or weak? Are there many of them or only a few?
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 Is the land where they're living good or bad? Are their towns like open camps, or do they have defensive walls?
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 Is the soil productive or not? Is it forested? Be brave, and bring back some of the country's fruit.” (It was the beginning of the grape harvest.)
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 So the men went and explored the land all the way from the Desert of Zin to Rehob, bear Lebo-hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 They went through the Negev and arrived in Hebron where Ahiman, Sheshai, and Talmai, the descendants of Anak, lived. This town was built seven years before the Egyptian town of Zoan.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 When they arrived at the Valley of Eshcol they chopped down a branch that had just one bunch of grapes. They had to carry it on a pole held between two men. They also collected some pomegranates and figs.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 (The place was named the Valley of Eshcol because of the bunch of grapes they took from there.)
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 Forty days later the men returned from exploring the country.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 They went to see Moses and Aaron, and all the Israelites gathered there at their camp in Kadesh in the Desert of Paran. They gave a report before everyone and showed them the fruit they had brought back from the country.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 This is the report they gave to Moses: “We went and explored the country you sent us to, and it is definitely very productive, as if it was flowing with milk and honey. Just look at some of its fruit!
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 But the people living there are strong, and their towns are big and have defensive walls. We also saw some descendants of Anak there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 The Amalekites live in the Negev. The Hittites, Jebusites, and the Amorites live in the hill country. The Canaanites live on the sea coast and also beside the Jordan.”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Then Caleb asked for quiet as the people stood before Moses and told them, “Let's go and take over the land. We can conquer the country, no doubt about it!”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 But the men who had gone with him disagreed. “We can't go and fight these people! They're much stronger than us!”
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 They spread a negative report among the Israelites about the country they had explored. They told people, “The country we explored destroys the people that live there. Plus everyone we saw was really big!
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 We even saw giants there—people descended from Anak the giant! Compared to them we looked like grasshoppers, and we must have looked like that to them too!”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”