< Nahum 1 >

1 A prophecy about Nineveh: the scroll of the vision that came to Nahum the Elkoshite.
Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
2 The Lord is a jealous and avenging God—the Lord God is avenging and angry. The Lord takes vengeance on his enemies, he is angry with those who are hostile to him.
Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
3 The Lord is slow to become angry, has great power, and will not leave the guilty unpunished. He walks among the whirlwind and the storm; the clouds are like dust beneath his feet.
Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
4 He commands the sea and makes it dry; he dries up all the rivers. Bashan and Carmel wither; the blossom of Lebanon fades.
Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
5 Mountains quake in his presence; hills melt away. The earth trembles before him—the whole world and everyone who lives there.
Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
6 Who can withstand his fury? Who can endure the heat of his anger? His rage pours out like molten fire; he shatters rocks to pieces.
Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
7 The Lord is good, a place of safety in a time of trouble. He takes care of those who place their trust in him,
Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
8 but those who oppose him will be swept away by a tremendous flood to their destruction. He pursues his enemies into the darkness of death.
amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
9 Why are you plotting against the Lord? He will end it completely; misery won't arise twice.
Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
10 They entangle themselves like people caught in thorn bushes; they are like drunks full of drink. They will be completely burned up like dry straw.
Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
11 One of you is plotting evil against the Lord, someone who is planning wickedness.
Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
12 This is what the Lord says: Even though they are strong and numerous, they will be cut down and they will pass away. Though I have caused you trouble, I will not do so anymore.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
13 Now I will break their yoke from your necks and tear away the chains which bind you.
Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
14 This is what the Lord has ordered concerning you. You will have no descendants to carry on your name. I will destroy the gods in your temples, all the wooden and metal idols. I am digging your grave, for you are depraved.
Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
15 Look! A messenger is coming over the mountains, bringing good news and proclaiming peace. Judah, celebrate your religious festivals and keep your vows, for never again will wicked enemies invade your land—they will be completely destroyed.
Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.

< Nahum 1 >