< Micah 1 >
1 Here is the message that the Lord gave to Micah of Moresheth at the time when Jotham, Ahaz, and Hezekiah were kings of Judah. This is what he saw concerning Samaria and Jerusalem.
Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
2 Listen, all the nations! Pay attention, everyone on earth! The Lord God testifies against you from the Lord's holy Temple.
Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
3 Look! The Lord is coming, leaving his place and coming down, and is walking on the high places of the earth.
Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
4 The mountains melt beneath him, the valleys burst apart, like wax in front of a fire, like water rushing down a slope. All this is happening because of the rebellion of the descendants of Jacob, the sins of the people of Israel.
Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
5 What is the rebellion of the descendants of Jacob? Isn't it what is happening in Samaria? Where are the idolatrous high places of Judah? Aren't they right in Jerusalem?
Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
6 Therefore I will make Samaria a pile of rubble in a field, a place for planting vineyards. I will roll its stones down into the valley; I will lay bare its foundations.
“Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
7 All their carved idols will be smashed to pieces. All that was earned by their temple prostitutes will be burned. All of their idols will be destroyed, for what she collected through the earnings of temple prostitutes will be taken away and used to pay other temple prostitutes.
Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
8 Because of this I will weep and wail, I will walk barefoot and naked, and will howl like jackals and mourn like owls.
Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
9 Their wound cannot be healed, it has extended to Judah, and reached right to the gates of Jerusalem.
Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
10 Don't mention it in Gath; don't weep at all. People of Beth-le-aphrah, roll in the dust.
Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
11 Leave, people of Shaphir, naked and ashamed. People of Zanaan don't come out. People of Beth Ezel mourn, for you have lost your support.
Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
12 The people of Maroth wait anxiously for relief, but disaster has come down from the Lord on the gate of Jerusalem.
Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
13 Harness the team of horses to the chariot, you people of Lachish, because the sins of the people of Jerusalem began with you, for the sins of Israel were first found in you.
Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
14 Send your goodbye gifts to Moresheth. The town of Achzib is a deception to the kings of Israel.
Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
15 I will bring a conqueror to attack you, people of Moresheth. The leaders of Israel will go to Adullam.
Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
16 Shave your heads, for the children you love will be taken away; make yourselves as bald as a vulture, for they will be exiled far away from you.
Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.