< Matthew 7 >

1 Don't judge others, so that you won't be judged.
Kada ku yi hukunci, domin ku ma kada a hukunta ku. Domin da irin hukuncin da ku kan hukunta da shi za a hukunta ku.
2 For whatever standard you use to judge others will be used to judge you, and whatever measurement you use to measure others will be used to measure you.
Mudun da kukan auna, da shi za a auna maku.
3 Why do you see the speck that's in your brother's eye? Don't you notice the plank that's in your own eye?
Don me kake duban dan hakin da ke idon dan'uwanka, amma ba ka kula da gungumen da ke naka idon ba?
4 How can you say to your brother, ‘Let me take out that speck from your eye’ when you have a plank in your own eye?
Ko kuwa yaya za ka iya ce wa dan'uwanka, 'Bari in cire maka dan hakin da ke idon ka,' alhali ga gungume a cikin naka idon?
5 You're being hypocritical! First get rid of the plank that's in your own eye. Then you'll be able to see clearly to take out the speck from your brother's eye.
Kai munafiki! Ka fara cire gungumen da ke idonka, sa'annan za ka iya gani sosai yadda za ka cire dan hakin da ke idon dan'uwanka.
6 Don't give dogs what's holy. Don't throw your pearls to pigs. That way the pigs won't trample them underfoot, and the dogs won't turn and attack you.
Kada ku ba karnuka abin da ke tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa aladu, lu'u lu'anku. Idan ba haka ba za su tattake su a karkashin sawunsu, su kuma juyo su kekketa ku.
7 Ask, and it will be given to you; seek, and you will find; knock, and the door will be opened for you.
Roka, kuma za a ba ku. Nema, kuma za ku samu. Kwankwasa kuma za a bude maku.
8 Everyone who asks, receives; everyone who seeks, finds; and everyone who knocks has the door opened for them.
Ai duk wanda ya roka, zai karba, kuma duk wanda ya nema zai samu, wanda ya kwankwasa kuma za a bude masa.
9 Would any of you give your son a stone if he asked for bread?
Ko, kuwa wane mutum ne a cikin ku, dan sa zai roke shi gurasa, ya ba shi dutse?
10 Or if he asked for fish, would you give him a snake?
Ko kuwa in ya roke shi kifi, zai ba shi maciji?
11 So if even you who are evil know to give good things to your children, how much more will your heavenly Father give good things to those who ask him.
Saboda haka, idan ku da ku ke miyagu, kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga 'ya'yanku, ina kimanin yadda Ubanku na sama zai ba da abubuwa masu kyau ga duk wadanda suke rokon sa?
12 Treat others the way you want them to treat you. This sums up the law and the prophets.
Saboda haka, duk abinda ku ke so mutane su yi maku, ku ma sai ku yi masu, domin wannan shi ne dukan shari'a da koyarwar annabawa.
13 Enter by the narrow entrance. For the entrance is wide, and the way is broad that leads to destruction, and many travel that way.
Ku shiga ta matsattsiyar kofa, don kofar zuwa hallaka na da fadi, hanyar ta mai saukin bi ce, masu shiga ta cikin ta suna da yawa.
14 But the entrance is narrow, and the way is difficult that leads to life, and only a few find it.
Domin kofar zuwa rai matsattsiya ce, hanyar ta mai wuyar bi ce, masu samun ta kuwa kadan ne.
15 Watch out for false prophets who come wearing sheep's clothing, but who on the inside are vicious wolves.
Ku kula da annabawan karya, wadanda su kan zo maku da siffar tumaki, amma a gaskiya kyarketai ne masu warwashewa.
16 You can recognize them by their fruits. Do people harvest grapes from thorn bushes, or figs from thistles?
Za ku gane su ta irin ''ya'yansu. Mutane na cirar inabi a jikin kaya, ko kuwa baure a jikin sarkakkiya?
17 So every good tree produces good fruit, while a bad tree produces bad fruit.
Haka kowanne itace mai kyau yakan haifi kyawawan 'ya'ya, amma mummunan itace kuwa yakan haifi munanan 'ya'ya.
18 A good tree can't produce bad fruit, and a bad tree can't produce good fruit.
Kyakkyawan itace ba zai taba haifar da munanan 'ya'ya ba, haka kuma mummunan itace ba zai taba haifar da kyawawan 'ya'ya ba.
19 Every tree that doesn't produce good fruit is chopped down and thrown into the fire.
Duk itacen da ba ya ba da 'ya'ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta.
20 So you'll recognize them by their fruits.
Domin haka, ta irin 'ya'yansu za a gane su.
21 Not everyone who calls me ‘Lord, Lord’ will enter the kingdom of heaven—only those who do the will of my Father in heaven.
Ba duk mai ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ne, zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda ya yi nufin Ubana da yake cikin sama.
22 Many will say to me at the Day of Judgment, ‘Lord, Lord, didn't we prophesy in your name and drive out demons in your name, and perform many miracles in your name?’
A ranar nan da yawa za su ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ashe ba mu yi annabci da sunanka ba, ba mu fitar da aljanu da sunanka ba, ba mu kuma yi manyan ayyuka masu yawa da sunanka ba?'
23 Then I will tell them, ‘I never knew you. Leave me, you people who practice wickedness!’
Sa'annan zan ce masu 'Ni ban taba saninku ba! Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!'
24 Everyone that hears the words I say, and follows them, is like a wise man who built his house on solid rock.
Saboda haka, dukan wanda yake jin maganata, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidan sa a bisa dutse.
25 The rain poured down, and the floods rose, and the winds blew hard against the house, but it didn't fall down, because its foundations were on solid rock.
Da ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, iska ta taso ta buga gidan, amma bai fadi ba, domin an gina shi bisa dutse.
26 Everyone that hears the words I say, and doesn't follow them, is like a foolish man who built his house on the sand.
Amma duk wanda ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta ba, za a misalta shi da wawan mutum da ya gina gidansa a kan rairayi.
27 The rain poured down, and the floods rose, and the winds blew hard against the house, and it fell down—it totally collapsed.”
Ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, sai iska ta taso ta buga gidan. Sai kuma ya rushe, ya kuwa yi cikakkiyar ragargajewa.''
28 When Jesus finished explaining these things, the crowds were amazed at his teaching,
Ya zama sa'adda Yesu ya gama fadin wadannan maganganu, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa,
29 for he taught like someone with authority, and not like their religious teachers.
Domin yana koya masu da iko, ba kamar marubuta ba.

< Matthew 7 >