< Matthew 22 >

1 Jesus spoke to them using more illustrated stories.
Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
2 “The kingdom of heaven is like a king who organized a wedding celebration for his son,” Jesus explained.
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
3 “He sent out his servants to everyone who was invited to the wedding to tell them to come, but they refused.
Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
4 So he sent out more servants, with the instructions, ‘Tell those who are invited that I've prepared the wedding banquet. The bulls and fattened calves have been killed—everything's ready. So come to the wedding!’
Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
5 But they ignored the invitation and left. One went to his fields; another to take care of his business.
Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
6 The rest grabbed the king's servants, mistreated them, and killed them.
Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
7 The king became furious. He sent his soldiers to destroy those murderers and burn down their town.
Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8 Then the king said to his servants, ‘The wedding banquet is ready, but those who were invited didn't deserve to attend.
Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
9 Go into the streets and invite everyone you find to come to the wedding.’
Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
10 So the servants went out into the streets and brought back everyone they could find, both the good and the bad. The wedding hall was full.
Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11 But when the king came in to meet the guests, he noticed a man who didn't have a wedding robe on.
Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
12 He asked him, ‘My friend, how did you get in here without a wedding robe?’ The man had nothing to say.
Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13 Then the king told his servants, ‘Bind his hands and feet, and throw him out into the dark, where there'll be crying and grinding of teeth.’
Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
14 For many are invited, but few are chosen.”
Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
15 Then the Pharisees left and met together to plot how they could trap him by what he said.
Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
16 They sent their disciples to him, together with some of Herod's supporters. “Teacher, we know you are a honest man, and that you teach God's way is the truth,” they began. “You don't allow yourself to be influenced by anyone, and you don't care about rank or status.
Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
17 So let us know your opinion. Is it right to pay Caesar's taxes, or not?”
To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
18 Jesus knew their motives were evil. He asked them, “Why are you trying to trap me, you hypocrites?
Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
19 Show me the coin that is used to pay the tax.” They brought a denarius coin to him.
Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
20 “Whose image and whose title is inscribed here?” he asked them.
Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
21 “Caesar's,” they replied. “You should give back to Caesar what belongs to Caesar, and to God what belongs to God,” he told them.
Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
22 When they heard Jesus' answer they were stunned. They went away and left him.
Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23 Later the same day some Sadducees came to see him. (They are the ones who say there's no resurrection.)
A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
24 They asked him, “Teacher, Moses said that if a married man dies without having children, his brother should marry his widow and have children on behalf of his brother.
cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25 Well, once there were seven brothers here with us. The first married, and died, and since he had no children he left his widow to his brother.
Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
26 The same thing happened to the second and third husband, right up to the seventh.
Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
27 In the end the woman died too.
Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
28 So when the resurrection takes place, whose wife of the seven brothers will she be, for she married all of them?”
To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
29 Jesus replied, “Your mistake is you don't know Scripture or what God can do.
Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
30 For in the resurrection people don't marry, and they aren't given in marriage either—they're like the angels in heaven.
Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31 As for the resurrection of the dead—haven't you read what God said to you,
Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
32 ‘I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob’? He's not the God of the dead, but of the living.”
'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
33 When the crowds heard what he said, they were amazed at his teaching.
Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 When the Pharisees heard that he'd left the Sadducees speechless, they got together and went to ask some more questions.
Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
35 One of them, who was a legal expert, asked him a question to try to trap him:
Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
36 “Teacher, which is the greatest commandment in the law?”
“Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
37 Jesus told them, “‘Love the Lord your God in all you think, in all you feel, and in all you do.’
Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
38 This is the greatest commandment, the first commandment.
Wannan itace babbar doka ta farko.
39 The second is just like it, ‘Love your neighbor as yourself.’
Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
40 All biblical law and the writings of the prophets depend on these two commandments.”
Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
41 While the Pharisees were gathered there, Jesus asked them a question.
Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
42 “What do you think about the Messiah?” he asked. “Whose son is he?” “The son of David,” they replied.
Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
43 “But how can David under inspiration call him ‘Lord’?” Jesus asked them. “He says,
Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
44 ‘The Lord said to my Lord, sit down at my right hand until I defeat all your enemies.’
“Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
45 If David called him Lord, how can he be his son?”
Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
46 Nobody could answer him, and from then on nobody dared to ask him any more questions.
Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.

< Matthew 22 >