< Matthew 17 >

1 Six days later Jesus took Peter, James and his brother John, with him and they went up a high mountain to be by themselves.
Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
2 He was transformed in front of them. His face shone like the sun. His clothes turned white as light.
A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
3 Then suddenly Moses and Elijah appeared before them, talking together with Jesus.
Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
4 Peter spoke up, saying to Jesus, “Lord, it's really good to be here. If you want I'll make three shelters—one for you, one for Moses, and one for Elijah.”
Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
5 While he was still speaking, a bright cloud covered them. A voice came from the cloud, saying, “This is my son whom I love, who pleases me. Listen to him.”
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
6 When they heard this, the disciples fell down on their faces, absolutely terrified.
Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
7 Jesus went over to them and touched them. “Get up,” he told them. “Don't be afraid.”
Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 When they looked up they didn't see anybody there except Jesus.
Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
9 As they descended the mountain Jesus gave them strict instructions. “Don't tell anybody what you saw until the Son of man has risen from the dead,” he told them.
Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
10 “So why do the religious teachers say that Elijah has to come first?” his disciples asked.
Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
11 “It's true that Elijah comes to put everything in place,” Jesus replied,
Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
12 “but I tell you that Elijah has already come and yet people didn't recognize who he was. They did whatever they felt like to him. In the same way the Son of man will also suffer at their hands.”
Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
13 Then the disciples realized that Jesus was referring to John the Baptist.
Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
14 When they approached the crowd, a man came to Jesus, and kneeled before him.
Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
15 “Lord, please have mercy on my son,” he said. “He loses his mind and suffers such terrible fits that he often falls in the fire or into water.
Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
16 I brought him to your disciples but they couldn't heal him.”
Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
17 “You people refuse to trust me, and are so corrupt!” Jesus responded. “How long do I have to remain here with you? How long do I have to put up with you? Bring him here to me!”
Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
18 Jesus confronted the demon and it left the boy, and he was healed straight away.
Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
19 Later the disciples came to Jesus in private and asked him, “Why couldn't we drive it out?”
Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
20 “Because you don't trust enough,” Jesus told them. “I tell you, even if your trust was as small as a mustard seed, you could say to this mountain, ‘Move from here to there,’ and it would move. Nothing would be impossible for you.”
Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
22 As they were walking together through Galilee, Jesus told them, “The Son of man is going to be betrayed and people will have power over him.
Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
23 They will kill him, but on the third day he will rise again.” The disciples were filled with sadness.
Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
24 When they arrived at Capernaum, those who were in charge of collecting the half-shekel Temple tax came to Peter and asked him, “Your teacher does pay the half-shekel tax, doesn't he?”
Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
25 “Yes, of course,” Peter replied. When he returned to where they were staying, Jesus anticipated the issue. “What do you think, Simon?” Jesus asked him. “Do the kings of this world collect their taxes and duties from their own sons or from others?”
Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
26 “From others,” Peter replied. So Jesus told him, “In that case the sons are exempt.
Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
27 But to avoid giving offense to anyone, go to the lake, and throw out a fishing line with a hook. Pull in the first fish you catch, and when you open its mouth there you'll find a stater coin. Take the coin and give it to them for both me and you.”
Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”

< Matthew 17 >