< Matthew 13 >
1 Later that day Jesus left the house, and sat down to teach beside the lake.
A waccan rana Yesu ya fito daga gida ya zauna a gefen teku.
2 So many people gathered around him that he got into a boat and sat down there to teach, while all the crowds stood on the beach.
Taro mai yawan gaske kuwa suka kewaye shi, sai ya shiga cikin kwalekwale ya zauna. Dukan taron kuwa na tsaye a bakin tekun.
3 He explained many things to them, using stories as illustrations. “The sower went out to sow,” he began.
Sai Yesu ya fada masu abubuwa da yawa cikin misalai. Ya ce, “Wani mai shuka, ya tafi yayi shuka.
4 “As he was sowing, some of the seeds fell on the path. The birds came and ate them up.
Da yayi shukar, wadansu irin suka fadi a kan hanya, sai tsunsaye suka zo suka cinye su.
5 Other seeds fell on stony ground where there wasn't much earth where they sprouted quickly.
Wadansu irin kuwa suka fadi a kan duwatsu, wurin da babu kasa. Nan da nan sai suka tsira, domin kasar babu zurfi.
6 The sun rose and scorched them and they withered because they had no roots.
Amma da rana ta taso, sai suka yankwane domin ba su yi saiwa ba, suka kuwa bushe suka zube.
7 Other seeds fell among thorns that grew up and choked them.
Wasu irin kuwa suka fada a cikin kayayuwa. Kayayuwan kuwa suka shake su.
8 Still other seeds fell on good soil. They produced a harvest—some one hundred, some sixty, and some thirty times what had been planted.
Wasu irin kuwa suka fada a wuri mai kyau suka ba da tsaba, wani ya ba da dari, wasu sitin, wasu kuma talatin.
9 Anybody who has ears should be listening!”
Duk mai kunnen ji, bari ya ji.
10 The disciples came to Jesus and asked him, “Why do you use illustrations when you speak to the people?”
Almajiran suka zo suka ce ma Yesu, “Don me ka ke yi wa taron magana da misali?”
11 “You're privileged to have revealed to you the mysteries of the kingdom of heaven, but they're not given such insights,” Jesus replied.
Yesu ya amsa ya ce masu, “An baku 'yanci ku fahimci asiran mulkin sama, amma gare su ba a bayar ba.
12 “Those who already have will have more given to them, more than enough. But those who don't have, whatever they have will be taken away from them.
Domin wanda yake da shi, za a kara masa, zai kuma samu dayawan gaske. Amma duk wanda ba shi da shi, sai a dauke har ma abin da yake dashi.
13 That's why I speak to them in illustrations. For even though they see, they do not see; and even though they hear, they do not hear; nor do they understand.
Saboda haka na yi masu magana cikin misalai, amma ko da ya ke sun gani, duk da haka ba su gani ba. Kuma ko da yake sun ji, hakika ba su ji ba, balle ma su fahimta.
14 The prophecy of Isaiah is fulfilled in them: ‘Even though you hear, you won't understand, and even though you see, you won't perceive.
A gare su ne annabcin Ishaya ya cika, wanda yake cewa, “Game da sauraro zaku saurara, amma ba za ku fahimta ba. Game da gani kuma za ku kalla, amma ba za ku gane ba.
15 They have a hard-hearted attitude, they don't want to listen, and they've closed their eyes. If they didn't they might be able to see with their eyes, hear with their ears, and understand in their minds. Then they could return to me and I would heal them.’
Domin zuciyar mutanen nan ta duhunta, sun taurare ga saurare, kuma sun rufe idanunsu domin kada su gani da idanunsu, ko kuwa su ji da kunnuwansu, ko kuwa su fahimta da zukatansu, saboda su juyo kuma in warkar da su'.
16 Your eyes are blessed, for they see. Your ears are blessed too, for they hear.
Amma idanunku masu albarka ne, domin sun gani, haka ma kunnuwanku, domin sun ji.
17 I'm telling you, many prophets and good people longed to see what you're seeing, but didn't see it. They longed to hear what you're hearing, but didn't hear it.
Hakika ina gaya muku, annabawa da mutane dayawa masu aldalci sun yi marmarin ganin abin da kuka gani, amma ba su sami ganin su ba. Sun yi marmarin jin abin da kuka ji, ba su kuwa ji su ba.
18 So listen to the story of the sower.
Ku saurari misalin nan na mai shuka.
19 When people hear the message about the kingdom and don't understand it, the evil one comes along and rips out what was sown in them. This is what happens to the seeds sown on the path.
Idan wani ya ji maganar mulkin sama amma bai fahimce ta ba, sai mugun nan ya zo ya kwace abinda aka shuka a zuciyarsa. Wannan shine irin da aka shuka a kan hanya.
20 The seeds sown on stony ground are people who hear the message and happily accept it straight away.
Shi wanda aka shuka akan duwatsu, shine wanda ya ji maganar ya kuma karbe ta da murna nan da nan.
21 They last for a while, but because they don't have roots, when problems and troubles come, they quickly fall away.
Duk da haka, bai yi karfi cikin ta ba kuma nan ba da dadaiwa ba. Da wahala da tsanani suka taso saboda maganar, sai ya yi tuntube nan da nan.
22 The seeds sown among thorns are people who hear the message, but then life's worries and the temptation of money choke the message so that they become fruitless. (aiōn )
Shi wanda aka shuka a cikin kayayuwa wannan shine wanda ya ji maganar, amma dawainiyar duniya da kuma yaudarar dukiya suka shake maganar, sai ya kasa ba da 'ya'ya. (aiōn )
23 The seeds sown on good soil are people who hear the message, and understand it, and who produce a good harvest—some one hundred, some sixty, and some thirty times what was sown.”
Shi wanda aka shuka a kasa mai kyau, wannan shine wanda ya ji maganar, ya kuma fahimce ta. Wannan shine wanda ba da 'ya'ya da gaske; wadansu ribi dari, wadansu sittin, wasu kuma talatin.”
24 Then he told them another illustrated story: “The kingdom of heaven is like a farmer who sowed good seeds in his field.
Yesu ya sake ba su wani misali, yana cewa “Za a kwatanta mulkin sama da wani mutum wanda ya shuka iri mai kyau a gona.
25 But while his workers were sleeping, an enemy came and sowed weed seeds on top of the wheat. Then they left.
Amma da mutane suka yi barci, magabcin sa ya zo ya shuka ciyayi a cikin alkamar, ya kuwa yi tafiyarsa.
26 So when the wheat grew and produced ears of grain, the weeds also grew up.
Sa'adda suka yi toho suka kuma ba da tsaba, sai ciyayin suka bayyana.
27 The farmer's workers came and asked him, ‘Sir, didn't you sow good seeds in your field? Where did the weeds come from?’
Bayin mai gonar kuwa suka zo suka ce masa, maigida, ashe ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? ya ya aka yi ta kasance da ciyayi?
28 ‘Some enemy has done this,’ he replied. ‘Do you want us to go and pull up the weeds?’ they asked him.
Ya ce masu, “Magabci ne ya yi wannan”. Sai bayin suka ce masa, 'kana so mu je mu tuge su ne?'
29 ‘No,’ he answered, ‘as you pull up the weeds, you might uproot the wheat too.
Mai gonar ya ce, 'A'a, kada a garin tuge ciyayin, ku tuge tare da alkamar.
30 Let them both grow until harvest, and then at harvest-time I'll tell the reapers to first gather the weeds, tie them up into bundles and burn them, and then gather the wheat and store it in my barn.’”
Bari dukan su su girma tare har lokacin girbi, a lokacin girbin zan gaya wa masu girbin, “Ku tuge ciyayin da farko a daura su dami dami sai a kona su, amma a tara alkamar a kai rumbunana.'”
31 He gave them another illustration: “The kingdom of heaven is like a mustard seed that a farmer sowed in his field.
Sai Yesu ya sake yin magana da su cikin misalai, yana cewa “Za a kwatanta mulkin sama da kwayar mustad, wanda wani mutum ya shuka a lambunsa.
32 Even though it's the tiniest of seeds it grows much bigger than other plants. In fact it grows into a tree big enough for birds to roost in its branches.”
Wannan iri shine mafi kankanta cikin dukan iri. Amma bayan ya yi girma, sai ya fi dukan ganyaye dake lambun. Ya zama itace, har ma tsuntsayen sama su yi sheka a rassansa.”
33 He told them another illustrated story: “The kingdom of heaven is like yeast that a woman mixed with a large quantity of flour, until all the dough was raised.”
Yesu ya sake fada masu wani misali. “Za a kwatanta mulkin sama da yisti da mace takan dauka ta kwaba gari da shi mudu uku har sai ya yi kumburi.”
34 Jesus explained all these things to the crowds using illustrated stories—in fact he didn't speak to them without using stories.
Duk wadannan abubuwa Yesu ya fada wa taron cikin misalai. Babu abinda ya fada masu da ba a cikin misali ba.
35 This fulfilled the prophet's words: “I will speak using stories, and I will explain things hidden from the creation of the world.”
Wannan ya kasance ne domin abinda annabin ya fada ya zama gaskiya, da ya ce, “Zan buda bakina da misali. In fadi abubuwan da ke boye tun daga halittar duniya.”
36 Then he left the crowds and went into a house. His disciples came over to him, and asked him, “Please explain to us the story about the weeds in the field.”
Sai Yesu ya bar taron ya shiga cikin gida. Amajiransa suka zo wurin sa suka ce, “Ka fasarta mana misalan nan a kan ciyayin da ke gonar”
37 “The one who sows the good seed is the Son of man,” Jesus explained.
Yesu ya amsa kuma ya ce, “Shi wanda ya shuka iri mai kyau Dan Mutum ne.
38 “The field is the world. The good seeds are the children of the kingdom. The weed seeds are the children of the evil one.
Gonar kuwa duniya ce; iri mai kyau kuma sune 'ya'yan mulkin. Ciyayin kuma sune 'ya'yan mugun,
39 The enemy that sowed the weed seeds is the devil. The harvest is the end of the world. The reapers are angels. (aiōn )
magabcin da ya shuka su kuma shaidan ne. Girbin shine karshen duniya, kuma masu girbin sune mala'iku. (aiōn )
40 Just as the weeds are harvested and burned so it will be at the end of the world. (aiōn )
Saboda haka, kamar yadda aka tara ciyayin aka kona su da wuta, haka ma zai faru a karshen duniya. (aiōn )
41 The Son of man will send out his angels, and they will gather up every sinful thing and everyone who does evil,
Dan Mutum zai aiki mala'ikunsa, kuma su tara dukan abubuwan da ke sa zunubi daga cikin mulkinsa, da kuma wadanda su ka yi aikin mugunta.
42 and will throw them into the blazing furnace, where there will be weeping and grinding of teeth.
Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.
43 Then those who live right will shine like the sun in the kingdom of their father. Anybody with ears should be listening!
Sa'an nan ne mutane masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Bari mai kunnen ji, ya ji.
44 The kingdom of heaven is like treasure hidden in a field. A man found it, reburied it, and then full of joy went and sold all he had and bought that field.
Mulkin sama kamar dukiya ce da ke boye a gona. Mutum ya samu sai ya boye ta, ya tafi cikin murna, ya sayar da mallakarsa kuma ya sayi filin.
45 The kingdom of heaven is also like a trader looking for good pearls.
Haka ma za a kwatanta mulkin sama da wani attajiri mai neman Lu'ulu'ai masu daraja.
46 When he found the most expensive pearl ever he went and sold all he had and bought it.
Da ya sami lu'ulu'u daya mai darajar gaske, ya je ya sayar da dukan mallakarsa ya kuma saye shi.
47 Once more, the kingdom of heaven is like a fishing net thrown into the sea that caught all kinds of fish.
Haka kuma, za a kwatanta mulkin sama da taru da aka jefa cikin teku, ya kuwa tara hallitu iri-iri.
48 When it was full it was dragged ashore. The good fish were put into baskets while the bad ones were thrown away.
Da ya cika, sai masuntan suka jawo shi bakin tekun. Sai suka zauna suka tara kyawawan abubuwan a taska, amma munanan abubuwan, suka watsar da su.
49 That's the way it will be when the end of the world comes. The angels will go out and separate the evil people from the good, (aiōn )
Haka zai kasance a karshen duniya. Mala'iku za su zo su ware miyagu daga cikin masu adalci. (aiōn )
50 and throw them into the blazing furnace where there will be weeping and grinding of teeth.
Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.
51 Now do you understood everything?” “Yes,” they replied.
Kun fahimci dukan wadannan abubuwa? Amajiran suka ce da shi, “I”.
52 “Every religious teacher who's learned about the kingdom of heaven is like a house-owner who brings out from his storeroom both new and old treasures,” Jesus said.
Sai Yesu ya ce masu, “Saboda haka kowane malamin attaura da ya zama almajirin mulkin sama, yana kamar mutum mai gida wanda ya zaro tsoho da sobon abu daga taskarsa.”
53 After Jesus finished telling these stories, he left.
Daga nan, sa'adda Yesu ya kammala ba da wadanan misalai, sai ya tafi ya bar wurin.
54 He went back to his home town and taught in the synagogue there. People were amazed, and asked, “Where does he get his wisdom and miracles from?
Sai Yesu ya shiga yankinsa ya koyar da mutane a masujadarsu. Saboda haka suka yi mamaki suna cewa, “Daga ina wannan mutumin ya sami hikimarsa da al'ajibai?
55 Isn't this the carpenter's son? Isn't his mother's name Mary, and his brothers James, and Joseph, and Simon, and Judas?
Wannan mutumin ba dan masassakin nan ba ne? Ba kuma sunan mahaifiyarsa Maryamu ba? Ba Kuma 'yan'uwansa sune, Yakubu da Yusufu da Saminu da kuma Yahuza ba?
56 Don't his sisters live here among us? So where does he get all this from?”
Ba 'yan'uwansa mata na tare da mu ba? To daga ina wannan mutumin ya sami dukan wadannnan abubuwa?
57 And so they refused to believe in him. “A prophet is honored everywhere except in his homeland and in his family,” Jesus told them.
Suka bata rai saboda shi. Amma Yesu ya ce masu, “Ai annabi bai rasa daraja sai dai ko a garinsa da kuma cikin iyalinsa.
58 Since they failed to trust in him, he did not do many miracles there.
Kuma bai yi al'ajibai dayawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.