< Mark 8 >
1 Around this time there was another large crowd that had nothing to eat. Jesus called the disciples together and told them,
A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
2 “I feel for the crowd because they have already stayed with me for three days and they have nothing to eat.
“Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
3 If I send them home without food, they'll faint on the way. Some have come from a long way away.”
In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
4 “Where could anybody find enough bread to feed them here in this wilderness?” answered his disciples.
Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
5 “How many loaves do you have?” he asked. “Seven,” they replied.
Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
6 He told the crowd to sit down on the ground. Then he took the seven loaves of bread, and gave thanks. He broke the bread and handed the pieces to his disciples to give to the crowd.
Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
7 They had a few fish as well, so having blessed them, he said, “Take these and share them too.”
Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
8 They ate until they were full, and then collected up seven baskets of leftovers.
Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
9 There were four thousand people there. After sending them on their way,
Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
10 Jesus climbed into a boat with his disciples and went to the region of Dalmanutha.
sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
11 The Pharisees arrived and began to argue with him, wanting him to give them a miraculous sign from heaven, trying to get him to prove himself.
Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
12 Jesus sighed deeply, and asked, “Why do you people want a sign? I tell you the truth: I will not give you a sign.”
Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
13 So he left them behind, climbed into the boat, and went back across the lake.
Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
14 But the disciples had forgotten to bring bread with them. All they had in the boat was one loaf.
Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
15 “Watch out—beware of the yeast of the Pharisees and of Herod!” he warned them.
Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
16 “He's saying that because we don't have any bread,” they concluded.
Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
17 Jesus knew what they were saying, and said, “Why are you talking about not having any bread? Are you still not thinking and not understanding? Have you closed your minds?
Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
18 You've got eyes to see, haven't you? And ears to hear?
Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
19 Don't you remember when I shared five loaves among five thousand? How many basketfuls of leftovers did you pick up?” “Twelve,” they replied.
Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
20 “And the seven loaves divided among four thousand. How many basketfuls of leftovers did you pick up?” “Seven,” they answered.
“Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
21 “Do you still not understand?” he asked them.
Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
22 They went to Bethsaida where some people brought a blind man to Jesus. They begged Jesus to touch him and heal him.
Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
23 Jesus took the blind man by the hand and took him outside the village. Jesus spat on the man's eyes and touched him with his hands. Then Jesus asked him, “Can you see anything?”
Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
24 The man looked around, and said, “I can see people, but they look like trees walking.”
Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
25 So Jesus touched the man's eyes again. He could see properly—he was cured and his sight was clear.
Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
26 Jesus sent the man home, and told him, “Don't go back through the village.”
Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
27 Jesus and his disciples left to go to the villages of Caesarea Philippi. On the way he asked his disciples, “Who do people say I am?”
Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
28 “Some say John the Baptist, some say Elijah, others say one of the prophets,” they replied.
Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
29 “But who do you say I am?” he asked them. “You are the Messiah!” Peter answered.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
30 Jesus warned them not to tell anybody about him.
Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
31 Then Jesus began to explain to them that the Son of man would suffer many things and be rejected by the elders, chief priests, and religious teachers. He would be killed, but three days later would rise again.
Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
32 Jesus explained this to them very clearly. But Peter took Jesus aside and started to reprimand him for what he said.
Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
33 Jesus turned around and looking at his disciples, reprimanded Peter. “Get away from me, Satan,” he said. “You're not thinking as God thinks, but as human beings do.”
Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
34 Jesus called the crowd and his disciples over to him, and told them, “If you want to follow me, you must give up on yourselves, pick up your cross and follow me.
Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
35 If you want to save your life you will lose it, but if you lose your life because of me and the good news you will save it.
Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
36 What use is it for you to gain everything in the whole world, and lose your life?
Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
37 What would you give in exchange for your life?
Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
38 If you're ashamed to acknowledge me and what I say among this unfaithful and sinful people, then the Son of man will be ashamed to acknowledge you when he comes with his Father's glory with the holy angels.”
Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”