< Mark 2 >

1 A few days later Jesus returned home to Capernaum, and news spread that he was there.
Da ya dawo Kafarnahum bayan yan kwanaki kadan, aka ji cewa yana gida.
2 So many people crowded inside the house that it was packed, even outside the door, as Jesus told them the message.
Da yawa suka taru a can, ba wuri har kofa, sai Yesu ya yi masu magana.
3 Four men had brought a man who was paralyzed,
Sai wadansu mutane su ka zo wurinsa dauke da wuni mutum shanyayye, mutane hudu na dauke da shi.
4 but they could not get near Jesus because of the crowds. So they went up on the roof and took it apart. After they had made an opening above Jesus, they lowered down the mat with the paralyzed man lying on it.
Lokacin da ba su iya zuwa kusa da shi ba domin yawan jama'a, sai su ka daye jinkar dakin daidai da inda ya ke. Bayan da suka huda ramin suka saukar da gado wanda shanyayyen ke kwance a kai.
5 When Jesus saw the trust these men had, Jesus said to the paralyzed man, “Friend, your sins are forgiven.”
Da ganin bangaskiyarsu, Yesu ya ce wa shanyayyen mutumin, “Da, an gafarta maka zunuban ka”.
6 Some of the religious teachers sitting there thought to themselves,
Amma wadansu marubuta da ke zaune a nan, suka yi tunani aransu.
7 “Why is he talking like this? He is blaspheming! Who can forgive sins? Only God can do that!”
Yaya wannan mutum zai yi magana haka? Ya yi sabo! wa ke iya gafarta zunubi “sai Allah kadai?”
8 Jesus knew right away what they were thinking. He said to them, “Why are you thinking like this?
Nan da nan Yesu ya sani a ruhunsa, abinda suke tunani a tsakaninsu. Ya ce masu, “Me ya sa kuke tunanin wannan a zuciyarku?
9 What's easier: to say to the paralyzed man, ‘Your sins are forgiven,’ or ‘Get up, pick up your mat, and walk’?
Me yafi sauki a cewa shanyayyen mutumin, 'An gafarta maka zunuban ka' ko kwa a ce masa, 'tashi, ka dauki shinfidarka, ka yi tafiyarka'?
10 But to convince you that the Son of man has the right to forgive sins,
Amma domin ku san cewa Dan mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya, ya ce wa shanyayyen,
11 I say to you (the paralyzed man), ‘Get up, pick up your mat, and go home.’”
''Na ce maka, tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidan ka.”
12 He stood up, picked up his mat, and walked out in front of everyone there. They were all amazed, and praised God, saying “We've never ever seen anything like this!”
Sai nan da nan ya tashi ya dauki tabarmarsa, ya fita gidan a gabansu, dukansu su ka yi mamaki, su ka girmama Allah, ''suka ce ba mu taba ganin abu irin wannan ba.”
13 Jesus went out beside the sea once more and taught the crowds that came to him.
Ya sake fita gefen tafki, dukan taron jama'a suka zo wurinsa, sai ya koya masu.
14 As he walked along, he saw Levi son of Alphaeus sitting at the tax-collector's booth. “Follow me,” Jesus told him. Levi got up and followed Jesus.
Sa'adda ya na wucewa, ya ga Levi dan Halfa yana zaune a wurin karbar haraji, sai ya ce masa, “Ka biyo ni.” Ya tashi, ya bi shi.
15 That evening Jesus ate dinner at Levi's house. Many tax collectors and “sinners” joined Jesus and his disciples for the meal, for there were many of these people that followed Jesus.
Sa'adda Yesu ya shiga gidan Levi yana cin abinci, masu karbar haraji da masu zunubi da yawa su ka zo wurinsa da almajiransa, jama'a masu yawan gaske suka ka bi shi.
16 When the religious leaders of the Pharisees saw Jesus eating with such people, they asked Jesus' disciples, “Why does he eat with tax collectors and sinners?”
Da Marubuta wadanda su ke Farisawa, sun ga cewa Yesu na cin abinci da masu zunubi da masu karbar haraji, sai su ka ce wa almajiransa, “Me ya sa ya ke ci da masu karbar haraji da mutane masu zunubi?”
17 When Jesus heard this, he told them, “It's not healthy people who need a doctor, but those who are sick. I haven't come to invite those who live right, but those who don't—the sinners.”
Da Yesu ya ji wannan ya ce masu, “Mutane wadanda ke da lafiya a jiki ba su bukatar likita; sai dai ko marasa lafiya ke bukatarsa. Ban zo domin in kira mutane masu a dalci ba, amma mutane masu zunubi.”
18 Now John's disciples and the Pharisees were fasting. Some of them came to Jesus, and asked him, “Why is it that John's disciples and the Pharisees fast, but your disciples don't?”
Almajiran Yahaya da Farisawa suna azumi, sai wadansu mutane suka zo suka ce, “Don me almajiran Yahaya da almajiran Farisawa na azumi amma na ka almajiran ba su yi?”
19 “Do wedding guests fast while the bridegroom is with them?” Jesus asked them. “No. While the bridegroom's with them, they can't fast.
Sai Yesu yace masu, “Abokan ango, za su yi azumi sa'adda ango yake tare da su? muddin suna tare da ango ba za su yi azumi ba.
20 But the day is coming when the bridegroom will be taken from them, and then they'll fast.
Amma kwanaki za su zo da za a dauki angon daga gare su, a wadancan kwanakin ne, za su yi azumi.
21 No one puts a patch that's not shrunk on old clothes. Otherwise the new piece will shrink away from the old, and make the tear worse.
Babu wanda zai dinka sabuwar riga ya hada ta da tsohuwar riga, sai rigar ta yage, kuma ta yi mummunar yagewa.
22 No one puts new wine in old wineskins. Otherwise the wine will burst the wineskins, and both the wine and wineskins will be wasted. No. You put new wine in new wineskins.”
Babu wanda zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsohuwar salka, ai sai salkar ta fashe kuma ruwan inabin ya zube. duka biyu ruwan inabin da salkar arasa su. A maimakon haka, sai ka sanya sabon ruwan inabi cikin sabuwar salka.”
23 One Sabbath day as Jesus was walking through the grain fields, his disciples started picking heads of grain as they walked along.
A ranar asabar Yesu ya tafi cikin gonakin hatsi, sai almajiransa su ka fara zagar hatsi,
24 The Pharisees asked Jesus, “Look, why are they doing what is not permitted on the Sabbath?”
Sai Farisawa su ka ce masa, “Duba, don me suke yin abin da bai dace a yi ranar Asabar ba?”
25 “Haven't you ever read what David did when he and his men were hungry and in need?” Jesus asked them.
Yace masu, Ba ku karanta ba abinda Dauda ya yi sa'adda yake jin yunwa, shi da mutanen da ke tare da shi?
26 “He went into God's house when Abiathar was high priest, and ate the consecrated bread which no one except the priests are permitted to eat, and gave it to his men too.”
Yadda ya shiga gidan Ubangiji, sa'adda Abiyata ya ke babban firist, ya ci gurasa da ke ta firist wadda bai dace wani ya ci ba sai Firistoci. Har kuma ya ba wadanda ke tare da shi.”
27 “The Sabbath was made for your benefit, not for you to benefit the Sabbath,” he told them.
Yesu yace, “Asabar an yi ta don mutum ne, ba a yi mutum don Asabar ba.
28 “So the Son of man is Lord even of the Sabbath.”
Saboda haka, Dan Mutum Ubangiji ne, har da na Asabar.”

< Mark 2 >