< Luke 3 >
1 By now Tiberias had been Caesar for fifteen years. Pontius Pilate was governor of Judea. Herod was ruler of Galilee, his brother Philip was ruler of Iturea and Trachonitis, and Lysanius was ruler of Abiline.
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 Annas and Caiphas were the current high priests. This was the time when the word of God came to John, Zechariah's son, who was living in the desert.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 He went throughout the whole Jordan region, announcing to everyone that they needed to be baptized to show they had repented and their sins had been forgiven.
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 As Isaiah the prophet wrote: “A voice was heard crying out in the desert, ‘Prepare the way of the Lord: make his paths straight.
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Every valley will be filled, and every mountain and hill will be leveled. Crooked ways will be straightened, and rough roads will be smoothed.
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 Every human being will see God's salvation.’”
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 John addressed the crowds that came to him to be baptized. “You viper's brood! Who warned you to flee from the coming judgment?” he asked.
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 “Demonstrate that you have truly repented. Don't try to justify yourselves by saying, ‘We're Abraham's descendants.’ Let me tell you, God can create children of Abraham from these stones.
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 The ax is set to begin chopping at the base of the trees. Any tree that doesn't produce good fruit will be chopped down and thrown into the fire.”
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 “So what should we do?” the crowds asked him.
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 “If you have two coats, then share with someone who doesn't have one. If you have food, then share with those who don't,” he told them.
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 Some tax collectors came to be baptized. “Teacher, what should we do?” they also asked.
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 “Don't collect any more tax than you're meant to,” he replied.
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 “What about us?” some soldiers asked. “What should we do?” “Don't demand money with threats of violence. Don't make accusations that are untrue. Be satisfied with your wages,” he replied.
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 The people were waiting expectantly, and wondered whether John himself might be the Messiah.
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 John replied and explained to everybody, “Yes, I am baptizing you in water. But the one who is coming is more important than me, and I'm not worthy to undo his sandals. He will baptize you with the Holy Spirit and with fire.
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 His winnowing fork is in his hand and he's ready to separate the wheat from the chaff on his threshing floor. He'll gather the wheat into his barn, but he will burn up the chaff with fire that can't be extinguished.”
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 John gave many warnings like this as he announced the good news to the people.
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 But when John reprimanded Herod the ruler for marrying Herodias, Herod's brother's wife, and for all the evil things he'd done,
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 Herod added to his crimes by having John thrown into jail.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 Now it happened that after everyone had been baptized, Jesus was baptized as well. As he was praying, heaven was opened,
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 and the Holy Spirit descended upon him, taking the form of a dove. A voice came from heaven, saying, “You are my son, the one I love. I am truly pleased with you.”
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 Jesus was around thirty when he began his public ministry. People presumed he was the son of Joseph. Joseph was the son of Heli,
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 the son of Matthat, the son of Levi, the son of Melchi, the son of Jannai, the son of Joseph,
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 the son of Mattathias, the son of Amos, the son of Nahum, the son of Esli, the son of Naggai,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 the son of Maath, the son of Mattathias, the son of Semein, the son of Josech, the son of Joda,
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 the son of Joanan, the son of Rhesa, the son of Zerubbabel, the son of Shealtiel, the son of Neri,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 the son of Melchi, the son of Addi, the son of Cosam, the son of Elmadam, the son of Er,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 the son of Joshua, the son of Eliezer, the son of Jorim, the son of Matthat, the son of Levi,
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 the son of Simeon, the son of Judah, the son of Joseph, the son of Jonam, the son of Eliakim,
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 the son of Melea, the son of Menna, the son of Mattatha, the son of Nathan, the son of David,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 the son of Jesse, the son of Obed, the son of Boaz, the son of Salmon, the son of Nahshon,
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 the son of Amminadab, the son of Arni, the son of Hezron, the son of Perez, the son of Judah,
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 the son of Jacob, the son of Isaac, the son of Abraham, the son of Terah, the son of Nahor,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 the son of Serug, the son of Reu, the son of Peleg, the son of Eber, the son of Shelah,
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 the son of Cainan, the son of Arphaxad, the son of Shem, the son of Noah, the son of Lamech,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 the son of Methuselah, the son of Enoch, the son of Jared, the son of Mahalaleel, the son of Cainan,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 the son of Enosh, the son of Seth, the son of Adam, the son of God.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.