< Luke 24 >
1 Very early on the first day of the week, the women went to the tomb, taking the spices they'd prepared.
Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
2 They found that the stone had been rolled away from the entrance to the tomb,
Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
3 but when they went in they didn't find the body of the Lord Jesus.
Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
4 While they were wondering what was going on, two men suddenly appeared dressed in clothes that shone brilliantly.
Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
5 The women were terrified and bowed down, their faces on the ground. They said to the women, “Why are you looking for someone who is alive among the dead?
Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
6 He's not here; he's risen from the dead! Remember what he told you while you were still in Galilee:
Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
7 ‘The Son of man must be betrayed into the hands of evil men, be crucified, and on the third day rise again.’”
cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
8 Then they remembered what he'd said.
Sai matan suka tuna da kalmominsa,
9 When they returned from the tomb they reported all that had happened to the eleven disciples and to all the others.
suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
10 Those who told the apostles what had happened were Mary Magdalene, Joanna, Mary the mother of James, and other women with them.
Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
11 But it seemed like nonsense to them, so they didn't believe the women.
Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
12 However, Peter got up and ran to the tomb. Bending down, he looked in and saw only the linen grave-clothes. So he went back home, wondering what had happened.
Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
13 The same day two disciples were on their way to a village called Emmaus, about seven miles from Jerusalem.
A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
14 They were talking about all that had happened.
Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
15 As they discussed and debated, Jesus came up and fell into step with them.
Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
16 But they were kept from recognizing him.
Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
17 “What are you discussing as you walk along?” he asked them. They stopped, their faces sad.
Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
18 One of them, called Cleopas, replied, “Are you just visiting Jerusalem? You must be the only person who doesn't know the things that have happened in the past few days.”
Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
19 “What things?” Jesus asked. “About Jesus of Nazareth,” they replied. “He was a prophet who spoke powerfully and performed great miracles before God and all the people.
Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
20 But our high priests and leaders handed him over to be condemned to death, and they crucified him.
Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
21 We had hoped he was the one who was going to rescue Israel. It's been three days now since all this happened.
Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
22 But then some of the women in our group surprised us.
Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
23 At dawn they went to the tomb and they didn't find his body. They came back saying that they'd seen a vision of angels who told them he's alive.
Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
24 Some of us went to the tomb, and found it just as the women said—but they didn't see him.”
Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
25 Jesus told them, “You're so dull! How slow you are to trust in all that the prophets said!
Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
26 Didn't the Messiah have to suffer before he could enter into his glory?”
Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
27 Then, starting with Moses and all the prophets, he explained to them everything that was said in Scripture about himself.
Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
28 As they approached the village they were going to, Jesus made it seem as if he was going farther.
Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
29 But they urged him, saying, “Please come and stay with us. It's getting late—the day is almost over.” So he went to stay with them.
Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
30 When he sat down to eat with them, he took the bread and gave thanks, broke it, and gave it to them.
Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
31 Their eyes were opened, and they recognized him. Then he disappeared from view.
Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
32 The two disciples said to each other, “Weren't our thoughts on fire when he spoke to us, as he explained the Scriptures to us?”
Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
33 They got up right away and returned to Jerusalem. There they found the eleven disciples and those who were with them meeting together,
Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
34 who said, “The Lord has really risen again! He has appeared to Simon.”
cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
35 Then those who had just arrived explained to the other disciples what had happened to them on the road, and how they had recognized Jesus when he broke bread.
Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
36 While they were talking, Jesus himself stood among them, and said, “Peace to you!”
Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
37 They were startled and afraid, thinking they were seeing a ghost.
Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
38 “Why are you frightened? Why are you doubting?” he asked them.
Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
39 “Look at my hands and my feet—you can see it's me. Touch me and you'll be certain, for a spirit doesn't have flesh and bones, as you see I have.”
Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
40 Having said this, he showed them his hands and feet.
Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
41 But they still couldn't believe it because they were so elated and amazed. He asked them, “Do you have anything to eat?”
Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
42 They gave him a piece of cooked fish,
Sai suka bashi gasasshen kifi.
43 and he took it and ate it in front of them.
Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
44 Then Jesus said to them, “This is what I explained to you while I was still with you. Everything written about me in the law of Moses, the prophets, and the psalms, had to be fulfilled.”
Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
45 Then he opened their minds so they were able to understand the Scriptures.
Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
46 He told them, “It was written like this: the Messiah would suffer and rise from the dead on the third day, and in his name
Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
47 repentance for the forgiveness of sins would be preached to all nations, beginning in Jerusalem.
Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
48 You are witnesses of all this.
Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
49 Now I'm going to send you what my Father promised—but wait in the city until you receive power from heaven.”
Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
50 Then he led them out until they were near Bethany, and lifting up his hands, he blessed them.
Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
51 While he was blessing them, he left them, and was taken up to heaven.
Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
52 They worshiped him, and then they returned to Jerusalem full of joy.
Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
53 They spent all their time in the Temple praising God.
Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.