< Luke 2 >

1 It was the time when Caesar Augustus issued a decree that there should be a census of everyone in the Roman Empire.
Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
2 This was the first census under governor Quirinius of Syria.
Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
3 So everybody went to their own city to be registered.
Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
4 Joseph was descended from King David, so he left Nazareth in Galilee to go to Bethlehem, the city of David, in Judea.
Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
5 He went to register there, together with Mary, who was pledged in marriage to him and expecting a baby.
Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6 While they were there, the time came for her to have her baby.
Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
7 She gave birth to her firstborn son. She wrapped him up in strips of cloth and laid him in a manger because the inn had no rooms left.
Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8 Nearby some shepherds were spending the night out in the fields, keeping watch over their flocks.
A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
9 An angel of the Lord appeared to them, and the glory of the Lord shone all around them. They were scared out of their wits!
Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10 “Don't be afraid!” the angel told them. “I'm here to bring you good news that will make the all the people really glad.
Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
11 The Savior has been born to you today, here in David's city. He is the Messiah, the Lord.
Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
12 You will recognize him by this sign: you will find the child wrapped in strips of cloth and lying in a manger.”
Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
13 Suddenly many heavenly beings appeared, praising God, saying,
Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
14 “Glory to the God of heaven, and on earth peace to those with whom he is pleased!”
“Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
15 After the angels had left them and returned to heaven, the shepherds said to one another, “Let's go to Bethlehem and see what's happened concerning these things the Lord has told us about.”
Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
16 They hurried there and found Mary, Joseph, and the baby, who was lying in the manger.
Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17 After they'd seen for themselves, they spread the news of what had happened and what they had been told about this baby.
Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
18 All those who heard about it were amazed at what the shepherds told them.
Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
19 But Mary was careful to remember all the things that had happened and often thought about them.
Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
20 The shepherds went back to watching their flocks, glorifying and thanking God for all that they'd heard and seen, for it was just as they'd been told.
Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21 After eight days, the time came for the baby to be circumcised, and he was named Jesus. This was the name given to him by the angel before he had even been conceived.
Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22 When the time of their purification according to the law of Moses was finished, Joseph and Mary took him to Jerusalem to present him to the Lord,
Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23 as the law of the Lord states, “Every firstborn son must be dedicated to the Lord.”
Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24 There they made a sacrifice, as God's law also states, of “a pair of turtle doves or two young pigeons.”
Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25 Living in Jerusalem at that time was a man called Simeon. Simeon did what was good and was very devout. He was waiting expectantly for the hope of Israel, and the Holy Spirit was upon him.
Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26 The Holy Spirit had shown him that he would not die before he saw the Lord's Messiah.
An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27 Following the Spirit's leading, he went to the Temple. When Jesus' parents brought in the little boy to be dedicated as required by the Law,
Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28 Simeon took Jesus in his arms, thanked God, and said,
sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29 “Lord and Master, now you can let your servant die in peace as you promised,
“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30 because I have seen for myself your salvation
Domin idanuna sun ga cetonka,
31 which you have prepared for everyone.
wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32 He is a light that will show you to the nations, the glory of your people Israel.”
Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33 Jesus' father and mother were shocked at what Simeon said about him.
Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34 Then Simeon blessed them, and said to Jesus' mother Mary, “This child is destined to cause many in Israel to fall and many to rise. He is a sign from God that many will reject,
Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35 revealing what they really think. For you it will feel like a sword piercing right though you.”
Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36 Anna the prophetess also lived in Jerusalem. She was the daughter of Phanuel of the tribe of Asher, and she was very old. She had been married for seven years,
Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
37 and then she had been widowed. She was eighty-four years old. She spent her time at the Temple in worship, fasting and praying.
sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
38 She came up to them right at that moment, and began praising God. She spoke about Jesus to all those who were looking forward to the time when God would set Jerusalem free.
A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39 Once they had completed everything God's law required, they returned to their home town of Nazareth in Galilee.
Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
40 The child grew strong, and was very wise. God's blessing was with him.
Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41 Jesus' parents traveled to Jerusalem every year for the Passover festival.
Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
42 When Jesus was twelve years old, they went to the festival as they always did.
Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
43 When the festival had finished and it was time to return home, the boy Jesus remained in Jerusalem, but his parents didn't realize this.
Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
44 They assumed he was with all the others traveling home. A day passed before they started looking for him among their friends and relatives.
Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45 When they couldn't find him they returned to Jerusalem to look for him there.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
46 It was three days before they found him in the Temple. He was sitting among the religious teachers, listening to them and asking them questions.
Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
47 All who heard him speak were surprised by his understanding and his answers.
Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48 His parents were totally confused when they saw what he was doing. His mother asked him, “Son, why have you treated us like this? Your father and I—we've been worried sick! We've been looking everywhere for you!”
Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
49 “Why is it that you were looking for me?” Jesus replied. “Didn't you know I should be here in my Father's house?”
Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 But they didn't understand what he meant.
Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51 Then he went back with them to Nazareth, and did what he was told. His mother kept a careful note of everything that happened.
Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
52 Jesus grew steadily wiser and stronger, favored both by God and by the people.
Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.

< Luke 2 >