< Judges 18 >
1 At that time Israel didn't have a king. The tribe of Dan was looking for territory where they could live, because up until then they hadn't gained possession of the land granted to them among the tribes of Israel.
To, a kwanakin nan Isra’ila ba ta da sarki. A kwanakin kuwa zuriyar Dan tana neman wurinsu na zama, gama ba su riga sun sami gādo tare da kabilan Isra’ila ba.
2 So the Danites chose from among them five leading men from Zorah and Eshtaol to scout out the land and explore it. “Go and explore the land,” they told them. When the men came to the hill country of Ephraim, they arrived at Micah's house where they spent the night.
Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
3 While they were there, they recognized the young Levite's accent, so they went to him and asked him, “So who brought you here, and what are you doing in this place? Why are you here?”
Sa’ad da suka yi kusa da gidan Mika, sai suka gane muryar saurayin nan Balawe; saboda haka suka shiga wurin suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan? Me ya sa kake a nan?”
4 “Micah arranged things for me, and he hired me as his priest,” he told them.
Ya gaya musu abin da Mika ya faɗa masa ya ce, “Ya ɗauke ni aiki ya kuma sa in zama masa firist.”
5 “Please ask the Lord for us so we can find out if our journey will be successful,” they asked him.
Sa’an nan suka ce masa, “Muna roƙonka ka nemi mana nufin Allah don mu sani ko tafiyarmu tana da nasara.”
6 “Go in peace,” the priest replied. “The journey you are taking is being observed by the Lord.”
Firist ya amsa ya ce, “Ku sauka lafiya, gama tafiyarku tana da yardan Ubangiji.”
7 The five men left and went to the town of Laish. They observed that the people there lived in safety, and followed the customs of the Sidonians. The people were unsuspecting and confident of their security, at home in a productive land. They didn't have a strong ruler, they lived a long way from the Sidonians, and had no other allies to help them.
Saboda haka mutum biyar ɗin suka tashi suka iso Layish, inda suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa, ba sa zato ga tsaro. Kuma da yake ƙasarsu ba ta bukata kome, suna da wadata. Suna kuma nesa da Sidoniyawa, ba sa kuma hulɗa da kowa.
8 The men returned to Zorah and Eshtaol, their relatives asked them, “What did you…?”
Da suka komo Zora da Eshtawol,’yan’uwansu suka tambaye su, “Me kuka gano?”
9 “Come on, let's go and attack them!” the men interrupted. “We've surveyed the land, and it's excellent! Aren't you going to do something? Don't put off going there and occupying the land!
Suka ce, “Ku zo mu yaƙe su! Mun ga ƙasar tana da kyau sosai. Ba za ku yi wani abu ba? Kada ku yi wata-wata, ku je kun mallaki ƙasar.
10 When you get there you'll find the people are unsuspecting and the land is extensive. God has given you a place where there's no shortage of anything!”
Sa’ad da kun kai can, za ku iske mutanen suna zama a sake, ƙasar kuwa mai faɗi ce wadda Allah ya sa a hannuwanku, ƙasar da ba tă rasa kome ba.”
11 So six hundred Danite armed men left Zorah and Eshtaol, ready to attack.
Sai mutane ɗari shida daga kabilar Dan suka yi ɗamarar yaƙi, suka tashi daga Zora da Eshtawol.
12 En route they camped at Kiriath-jearim in Judah. That's why the place west of Kiriath-jearim is called the Camp of Dan to this very day.
A kan hanyarsu suka kafa sansani kusa da Kiriyat Yeyarim a Yahuda. Shi ya sa a ana kira wurin nan yamma da Kiriyat Yeyarim Mahane Dan har wa yau.
13 Then they left from there and went into the hill country of Ephraim and came to Micah's house.
Daga can suka tafi ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika.
14 Then the five men who had gone to scout out the land of Laish told the other tribesmen, “Do you realize that here in these houses there's an ephod, household gods, and a carved idol, an image made with molten silver? So you know what you should do.”
Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
15 The five men left the road and went to where the young Levite was living in Micah's home to ask how he was.
Saboda haka suka juya a wurin suka shiga gidan saurayin nan Balawe a wajen Mika suka gaishe shi.
16 The six hundred Danite armed men stood at the entrance by the gate.
Mutanen Dan ɗari shida da suka sha ɗamarar yaƙi suka tsaya a bakin ƙofa.
17 The five men went inside and took the carved idol, the ephod, the household idols, and the image made with molten silver. The priest was standing by the gate with the six hundred armed men.
Sai mutum biyar da suka leƙi asirin ƙasar suka shiga ciki suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi yayinda firist ɗin tare da mutane ɗari shida da suka yi ɗamarar yaƙi suna tsaye a bakin ƙofa.
18 When the priest saw them taking all the religious objects from Micah's home, he asked them, “What are you doing?”
Sa’ad da waɗannan mutane suka shiga gidan Mika suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi, sai firist ya ce musu, “Me kuke yi?”
19 “Be quiet! Don't say anything! Come with us, and you can be our ‘father’ and priest. Wouldn't it be better for you if instead of being a priest for just one man's household that you were the priest of an Israelite tribe and family?”
Suka ce, “Ka yi shiru! Kada ka ce wani abu. Zo tare da mu, ka zama mahaifinmu da kuma firist. Bai fi maka ka yi wa kabila da kuma zuriya a Isra’ila aikin firist ba, da ka bauta wa iyali guda kawai?”
20 This seemed like a good idea to the priest and he left with them. Carrying the ephod, the household idols, and the image made with molten silver, he marched with the people all around him.
Sai firist ya yi farin ciki. Ya ɗauki efod, sauran allolin gida da siffar da aka sassaƙa ya tafi tare da mutanen.
21 They continued their journey, putting their children, livestock, and possessions ahead of them.
Suka sa’ya’yansu ƙanana a gaba, dabbobinsu da mallakansu a gabansu, suka juya suka tafi.
22 The Danites were already quite a way from Micah's home when men from Micah's village caught up with them,
Sa’ad da suka yi ɗan nisa daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da suke maƙwabtakar da Mika suka taru suka bi mutanen Dan suka cim musu.
23 shouting at them. The Danites turned around to face them and asked Micah, “What's the matter with you? Why call out these men to come after us?”
Da suna ihu suna binsu, sai mutanen Dan suka waiga suka cewa Mika, “Mece ce damuwarka da ka kira mutanenka su zo su fāɗa mana?”
24 “You stole the gods I made, and my priest too, and then left. What have you left me with? How can you ask me, ‘What's the matter with you?’”
Ya amsa ya ce, “Kun kwashe allolin da na yi, da kuma firist nawa, kuka tafi. Me kuma nake da shi? Yaya za ku ce, ‘Mece ce damuwata?’”
25 “Don't complain to us!” Danites replied. “Otherwise some hot-tempered people here might attack you and you and your family will lose your lives!”
Mutanen Dan suka ce, “Kada ka kuskura ka ce kome, in ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.”
26 The Danites carried on their way. Micah saw that they were too strong for him to fight so he turned around and went back home.
Saboda haka mutanen Dan suka kama hanyarsu, Mika kuwa da ya ga an fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida.
27 So the Danites took with them the idols that Micah had made, as well as his priest. They attacked Laish with its peaceful and unsuspecting people, killed them with swords, and burned down the town.
Sa’an nan suka ɗauko abin da Mika ya yi, da firist nasa, suka tafi Layish, suka fāɗa wa mutanen da suke zaman lafiya, ransu kuma a kwance. Suka fāɗa musu suka kuma ƙone birninsu.
28 No one could save them because they were a long way from Sidon and had no other allies to help them. The town was in the valley belonging to Beth-rehob. The Danites rebuilt the city and lived there.
Ba wanda zai cece su domin suna nesa da Bet-Sidon kuma ba sa hulɗa da kowa. Birnin yana a kwari kusa da Bet-Rekob. Mutanen Dan suka sāke gina birnin suka zauna a can.
29 They renamed the city Dan after their forefather, the son of Israel. Laish was its former name.
Suka sa wa birnin suna Dan, wato, sunan kakansu Dan, wanda aka haifa wa Isra’ila, ko da yake a dā ana kira birnin Layish.
30 The Danites erected the carved idol to worship, and Jonathan, son of Gershom, son of Moses, and his sons became priests for the tribe of Dan until the time when the people went into captivity from the land.
A can mutanen Dan suka kafa wa kansu gumaka, Yonatan ɗan Gershom, ɗan Musa, da’ya’yansa maza firistoci ne na kabilar Dan har lokacin da aka kwashe mutane zuwa bauta.
31 They worshiped the carved idol that Micah had made the whole time God's Temple was at Shiloh.
Suka ci gaba da amfani da gumakan da Mika ya yi, a duk wannan lokacin gidan Allah yana a Shilo.