< Joshua 4 >
1 Once the entire nation had finished crossing the Jordan, the Lord told Joshua,
Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 “Choose twelve men from the people, one per tribe,
“Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
3 and tell them, ‘Pick up twelve stones from the middle of the Jordan, from right where the priests are standing. Then carry them and set them down at the place where you will camp tonight.’”
ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
4 So Joshua sent for the twelve men he had chosen, one from each tribe,
Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
5 and told them, “Go back into the middle of the Jordan, right in front of the Ark of the Agreement of the Lord your God, and each of you pick up a stone and carry it on your shoulder, one for each of the tribes of Israel.
ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
6 This will be a memorial among you so when your children one day ask, ‘What do these stones mean?’
yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
7 you can tell them, ‘It's about the time the Jordan River stopped flowing when the Ark of the Lord's Agreement went across. When it crossed over the water stopped. These stones are a memorial to the people of Israel forever.’”
Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
8 The people of Israel did as Joshua told them. The men picked up twelve stones from the middle of the Jordan as the Lord had instructed Joshua. They carried them to the place where they camped overnight and placed the stones there, one for each of the tribes of Israel.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
9 Joshua also set up twelve stones in the middle of the Jordan right where the priests carrying the Ark of the Agreement had stood, and they are still there to this very day.
Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
10 The priests carrying the Ark remained standing in the middle of the Jordan until everything was done just as the Lord had told the people to do, all that Moses had told Joshua to do. The people crossed over quickly.
Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
11 Once all the people had crossed over, they watched as the Ark of the Lord was carried across by the priests.
Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
12 The armed men from the tribes of Reuben and Gad, and the half tribe of Manasseh crossed at the head of the people of Israel, as Moses had stipulated.
Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
13 They numbered about 40,000 men, armed and ready for battle, crossed in the presence of the Lord to the plains of Jericho.
Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
14 On that day the Lord confirmed Joshua as great leader in the sight of all the Israelites, and they were in awe of him just as they had been in awe of Moses.
A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
15 The Lord had told Joshua,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
16 “Order the priests carrying the Ark of the Testimony to come up out of the Jordan.”
“Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
17 So Joshua told the priests, “Come up out of the Jordan.”
Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
18 The priests came up out of the Jordan carrying the Ark of the Agreement, and as soon as their feet touched dry ground the waters of the Jordan returned to where they had been, overflowing its banks as before.
Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
19 The people went up from the Jordan and camped at Gilgal, to the east of Jericho, on the tenth day of the first month.
A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
20 Joshua set up at Gilgal the twelve stones that had been taken from the Jordan.
Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
21 He told the Israelites, “When some day your children ask you their parents, ‘What do these stones mean?’
Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
22 you can explain to them, ‘This is where the Israelites crossed the Jordan on dry ground.’
Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
23 For the Lord your God made the Jordan River dry up right in front of you so you all could cross, just as the Lord your God did at the Red Sea which he dried up so we could all cross.
Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
24 He did this so everyone on earth would know how powerful the Lord is, and so that you might be in awe of the Lord your God forever.”
Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”