< John 10 >

1 “I tell you the truth, anyone who doesn't come in through the gate of the sheepfold but climbs in some other way is a thief and a robber.
“Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi.
2 The one who comes in through the gate is the shepherd of the sheep.
Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.
3 The gatekeeper opens it for him, and the sheep respond to his voice. He calls his own sheep by name, and leads them out.
Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje.
4 After bringing them out, he walks ahead of them, and the sheep follow him because they recognize his voice.
Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.
5 They won't follow strangers. In fact they run away from a stranger because they don't recognize the voice of strangers.”
Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba.”
6 When Jesus gave this illustration those who were listening to him didn't understand what he meant.
Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.
7 So Jesus explained again, “I tell you the truth: I am the gate of the sheepfold.
Sai Yesu ya ce masu kuma, “Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki.
8 All those who came before me were thieves and robbers, but the sheep didn't listen to them.
Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.
9 I am the gate. Anyone who comes in through me will be healed. They will be able to come and go, and find the food they need.
Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo.
10 The thief comes only to steal, kill, and destroy. I've come to bring you life, life full to overflowing.
Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.
11 I am the good shepherd. The good shepherd lays down his life for the sheep.
Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa.
12 The man paid to look after the sheep is not the shepherd and he runs away when he sees the wolf coming. He abandons the sheep because they're not his, and the wolf attacks and scatters the flock
Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su.
13 for the man is only working for pay and doesn't care about the sheep.
Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.
14 I am the good shepherd. I know who are mine, and they know me,
Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni.
15 just as the Father knows me and I know him. I lay down my life for the sheep.
Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin.
16 I have other sheep that are not in this sheepfold. I must bring them too. They will listen to my voice and there will be one flock with one shepherd.
Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.
17 This is why the Father loves me, because I lay down my life so I may take it up again.
Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma.
18 No one takes it from me; I choose to lay it down. I have the right to give it up, and I have the right to take it back. This is the command my Father gave me.”
Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana.”
19 The Jews were again divided in their opinion about Jesus over these words.
Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin.
20 Many of them said, “He's demon-possessed! He's mad! Why are you listening to him?”
Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?”
21 Others said, “These aren't the words of someone who's demon-possessed. Besides, a demon can't open eyes that are blind.”
Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?”
22 It was winter, and the time of the Festival of Dedication in Jerusalem.
Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo.
23 Jesus was walking in the Temple through Solomon's porch. The Jews surrounded him, asking,
A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu.
24 “How long are you going to keep us hanging in suspense? If you are the Messiah then tell us plainly!”
Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, “Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla.”
25 Jesus replied, “I already told you but you refuse to believe it. The miracles I do in my Father's name prove who I am.
Yesu ya ce masu, “Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina.
26 You don't believe me because you are not my sheep.
Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 My sheep recognize my voice; I know them, and they follow me.
Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na.
28 I give them eternal life; they shall never be lost, and no one can snatch them from me. (aiōn g165, aiōnios g166)
Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 My Father who gave them to me is greater than anyone else; no one can snatch them from him.
Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban.
30 I and the Father are one.”
Ni da Uban daya ne.”
31 Once again the Jews picked up stones to stone him.
Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.
32 Jesus said to them, “You've seen many good deeds that I've done from the Father. Which one are you stoning me for?”
Yesu ya amsa masu, “Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?”
33 The Jews replied, “We're not stoning you for a good deed, but for blasphemy because you are just a man but you're claiming to be God.”
Sai Yahudawa suka amsa masa, “ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah.”
34 Jesus answered them, “Isn't it written in your law, ‘I said, you are gods’?
Yesu ya amsa masu, “Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, “ku alloli ne”'?”
35 He called those people ‘gods,’ the people to whom the word of God came—and Scripture can't be altered.
In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba),
36 So why are you saying the one whom the Father set apart and sent into the world is blaspheming because I said ‘I am the Son of God’?
kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?
37 If I'm not doing what my Father does, then don't believe me.
In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni.
38 But if that is what I'm doing, even though you don't believe me, you should believe because of the evidence of what I've done. That way you can know and understand that the Father is in me, and I am in the Father.”
Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban.”
39 Once again they tried to arrest him, but he escaped from them.
Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.
40 He went back across the Jordan River to the place where John had begun baptizing, and he stayed there.
Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin.
41 Many people came to him, and they said, “John didn't perform miracles, but everything he said about this man has come true.”
Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,”Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne.”
42 Many who were there put their trust in Jesus.
Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.

< John 10 >