< Joel 2 >

1 Blow the trumpet in Zion! Sound the alarm on my holy mountain! Let all who live in the land tremble for the day of the Lord is coming—it's definitely near!
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 It's a gloomy day of darkness, a day of thick clouds and heavy shadows. Like the dawn spreading over the mountains, an army appears, so large and powerful that there has never ever been anything like it before, nor will there ever be anything like it again.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Fire blazes in front of them, behind them flames are burning. In front of them the land looks like the Garden of Eden, behind them is a desert of total desolation: not a single survivor remains.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 They have the appearance of horses; they charge like cavalry.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Listen to the sound: they are like rumbling chariots leaping over the mountain tops, they are like crackling flames burning stubble, they are like a mighty army marching in formation into battle.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Terror seizes all those in their path; all the people's faces grow pale.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 They attack like mighty warriors; they scale walls like soldiers. They all march as one, never breaking ranks.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 They do not jostle one another, they stay on track; and even if some are cut down, they are not stopped.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 They rush to and fro in the city; they run along the walls; they climb into houses, entering through the windows like thieves.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 The earth quakes before them, the heavens tremble, the sun and the moon grow dark, the stars stop shining.
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 The Lord shouts his commands at the head of his army. His camp his immense, and those who carry out his orders are powerful. The day of the Lord is totally terrifying—who can stand it?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 “Yet even now,” says the Lord, “Come back to me while there is still time. Come to me with all your heart, with fasting and prayer.
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 Repent in your minds, and not by tearing your clothes.” Come back to the Lord your God for he is gracious and kind. He is slow to get angry and full of faithful love, and changes his mind about sending punishment.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Who knows? Maybe he will change his mind, leaving behind a blessing so that you will be able to make grain and wine offerings to the Lord your God.
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blow the trumpet in Zion! Proclaim a fast; call a solemn assembly.
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Gather the people together: the elders, the children, even the babies. Let the bridegroom leave his room; let the bride leave her room.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Let the priests, the ministers of the Lord, weep between the porch and the altar of the Temple. Let them say, “Lord, please take pity on your people, and do not let your inheritance be disgraced, ruled over by foreign nations, so that the people of these nations could ask, ‘Where is their God?’”
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 Now the Lord is very protective of his land and takes pity on his people.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 The Lord will reply, saying to his people, “Look! I am sending you grain and new wine and olive oil, and you will be satisfied. You will no longer be a disgrace among the foreign nations.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 I will remove from you the army from the north; I will drive them into the desolate wilderness—the front into the eastern sea, and the rear into the western sea. The stench of the dead army will rise up—a real stink—for it has done terrible things.”
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Don't be afraid, people of the land! Be happy and celebrate, for the Lord has done incredible things!
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Don't be afraid, wild animals! For the pastures of the wilderness are turning green. The trees are fruiting again—the fig trees and the grapevines are producing a good crop.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 People of Jerusalem! Celebrate and be happy in the Lord your God because he has given you rain to show his goodness. As before he sends the autumn and the spring rains.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 The threshing floors will be full of grain, the vats will overflow with new wine and olive oil.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 “I will give back to you what you lost over the years to the swarming, hopping, destroying, and cutting locusts, this great army that I sent against you.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 You will have plenty to eat, and you will be satisfied, and you will praise the name of the Lord your God who has done miracles for you. My people will never again be ashamed.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 You will know that I am in the midst of my people Israel, that I am the Lord your God, and that there is no other. My people will never again be ashamed.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 After this I will pour out my spirit on everyone. Your sons and daughters will be my prophets, your old men will dream dreams, and your young men will see visions.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 In those days I will also pour out my spirit on male slaves and female slaves.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 I will place wonders in the heavens and on earth: blood, and fire, and columns of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 The sun will turn dark, and the moon will turn red like blood at the coming of the great and fearful day of the Lord.”
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 Then everyone who calls on the name of the Lord will be saved, rescued from Mount Zion and Jerusalem, as the Lord has said—these are among the survivors the Lord has called.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joel 2 >