< Job 19 >
2 “How long will you go on tormenting me? How long will you go on crushing me with words?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Ten times already you have humiliated me. Aren't you ashamed for treating me so badly?
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Even if I did sin, that's my problem, and has nothing to do with you.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 You think you're so much better than me, and you use my degradation against me.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 But you should realize that it's God who has wronged me, he has trapped me in his net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Even though I cry for help, I get no answer; even though I shout my objections, I get no justice.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 God has walled me in so I can't escape; he has plunged my path into darkness.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He has stripped my honor from me; he has taken away my reputation.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He tears me down from all sides until I am finished; he has destroyed my hope like a tree that is uprooted.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 His anger burns against me; he treats me as one of his enemies.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 God's troops assemble to attack me. They build ramparts against me. They encircle and besiege my home.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He has driven my brothers far away from me; all my former friends are estranged from me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My relatives have abandoned me; my close friends have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 My house guests and my maidservants treat me as a stranger—to them I have become a foreigner.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I call my servant, but he doesn't reply. I have to beg him!
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 I am repulsive to my wife, and I am loathsome to my own brothers.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Even young children despise me; when I stand up they ridicule me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 All my closest friends despise me, and those I loved have turned on me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 I've been reduced to skin and bones and I survive by the skin of my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Have pity on me, my friends, have pity on me, because God has struck me down!
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why are you persecuting me like God does? Aren't you satisfied with getting your pound of flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 I wish my words could be written down, recorded in a book,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 or engraved with an iron pen and molten lead in the rock forever.
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 I know my Redeemer is alive, and that he shall finally take the stand for me on the earth.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 Even though my skin is destroyed, in my body I shall see God.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 I myself will see him—with my own eyes, and not those of someone else! The thought overcomes me!
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 You say to yourselves, ‘How can we make him suffer so he can see he is the source of his problems?’
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 You yourselves should fear being punished by God, for you know anger brings God's punishment that accompanies judgment.”
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”