< Job 18 >

1 Then Bildad the Shuhite spoke up and said,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “How long will you go on talking, hunting for the right words to say? Talk sense if you want us to reply!
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Do you think we're dumb animals? Do we look stupid to you?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 You tear yourself apart with your anger. Do you think the earth has to be abandoned, or the mountains moved, just because of you?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 It's certain that the life of the wicked will end like a lamp that is snuffed out—their flame will shine no more.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 The light in their home goes out, the lamp hanging above is extinguished.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Instead of taking strong strides they stumble, and their own plans cause them to fall.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Their own feet trip them up and they are caught in a net; as they walk along they fall into a pit.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 A trap grabs them by the heel; a snare tightens around them.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 A noose is hidden on the ground for them; a rope is stretched across the path to trip them.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Terrors scare the wicked, coming at them from every side, chasing them, biting at their heels.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Hunger robs them of strength; disaster waits for them when they fall.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Disease devours their skin; deadly disease consumes their limbs.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 They are torn from the homes they trusted in and taken to the king of terrors.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 People they don't know will live in their homes; sulfur will be scattered where they used to live.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 They wither away, roots below and branches above;
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 the memory of them fades from the earth; nobody remembers their names any more.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 They are thrown out of light into darkness, driven from the world.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 They have no children or descendants among their people, and no survivors where they used to live.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 People of the west are appalled at what happens to them. People of the east are shocked.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 This is what happens to the homes of the wicked, to the places of those who reject God.”
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >