< Job 14 >

1 Life is short and full of trouble,
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 like a flower that blooms and withers, like a passing shadow that soon disappears.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Do you even notice me, God, and why do you have to drag me to court?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Who can bring something clean of what is unclean? No one.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 You have determined how long we shall live—the number of months, a time limit on our lives.
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 So leave us alone and give us some peace—so like a laborer we could enjoy a few hours of rest at the end of the day.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 Even a tree that's cut down has the hope of sprouting again, of sending up shoots and continuing to live.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Even though its roots grow old in the earth, and its stump dies in the ground,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 just a trickle of water will make it bud and grow branches like a young plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But human beings die, their strength dwindles away; they perish, and where are they then?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 Like water evaporating from a lake and a river that dries up and disappears,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 so human beings lie down and don't get up again. Until the heavens cease to exist they will not awake from their sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 I wish you would hide me in Sheol; conceal me there until your anger is gone. Set a definite time for me there, and remember me! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 Will the dead live again? Then I would have hope through all my time of trouble until my release comes.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 You would call and I would answer you; you would long for me, the being that you made.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 Then you would look after me and wouldn't be watching me to see if I sinned.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 My sins would be sealed up in a bag and you would cover my guilt.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 But just as the mountains crumble and fall, and the rocks tumble down;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 as water wears away the stones, as floods wash away the soil, so you destroy the hope people have.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 You continually overpower them and they pass away; you distort their faces in death and send them away.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 Their children may become important or fall from their positions, but they don't know or see any of this.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 As people die they only know their own pain and are sad for themselves.”
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >