< Jeremiah 47 >

1 This is the message from the Lord that came to Jeremiah the prophet about the Philistines before Pharaoh attacked Gaza.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
2 This is what the Lord says: Look at the waters rising from the north! They will become an overflowing river that sweeps across the country and everything in it, flooding the towns and everyone's homes. The people will cry out for help; everyone who lives in the country will weep,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
3 as they hear the sound of stallions charging, the rattling of chariots and the rumble of their wheels. Fathers won't go back to help their sons—they have no strength because they're terrified.
da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
4 The day has arrived when all the Philistines will be destroyed, when Tyre and Sidon will have no more allies to help them. The Lord is going to destroy the Philistines, those who are left from the island of Crete.
Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
5 The people of Gaza will shave their heads; the town of Ashkelon lies in ruins. You who are left on the coastal plain, how long will you go on cutting yourself?
Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
6 Oh sword of the Lord, when are you going to stop killing? Go back in your sheath. Stop killing and stay there!
“Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
7 But how can the sword stop killing when the Lord has given it orders to attack Ashkelon and its coastlands?
Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

< Jeremiah 47 >