< Jeremiah 34 >

1 This is the Lord's message that came to Jeremiah when Nebuchadnezzar king of Babylon, all his army, along with troops from all the countries he ruled and other nations were attacking Jerusalem and all its nearby towns:
Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 This is what the Lord, the God of Israel, says: Go and talk to Zedekiah king of Judah and tell him that this is what the Lord says: Listen! I am about to hand this city over to the king of Babylon, and he is going to burn it down.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
3 You yourself won't escape being captured by him. You will certainly be taken prisoner and brought before him to speak with him personally and see him face to face. You will be taken to Babylon.
Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
4 Listen to what the Lord is telling you, Zedekiah king of Judah. This is what the Lord says about you: You won't be killed;
“‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
5 you will die in peace. You will have a proper funeral with incense burned for you as they did for your forefathers, the kings who ruled before you. They will weep for you, crying, “The king is dead.” I myself am telling you this, declares the Lord.
za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
6 Jeremiah the prophet told Zedekiah king of Judah all this there in Jerusalem.
Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
7 At this time the king of Babylon's army was attacking the city and the Judean towns of Lachish and Azekah. These were the only fortified cities that had not yet been conquered in Judah.
yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
8 A message from the Lord came to Jeremiah after King Zedekiah had made a agreement with everyone in Jerusalem to announce a proclamation of freedom.
Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
9 This meant that every slave owner should free their Hebrew slaves, both male and female. No one was to force their fellow citizens to remain slaves any longer.
Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
10 All the officials and all the people who accepted this agreement did what they said. They freed their male and female slaves, not forcing them to remain slaves any longer. They obeyed and let them go free.
Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
11 However, later on they changed their minds and took back the male and female slaves they'd freed, forcing them back into slavery.
Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
12 A message from the Lord came to Jeremiah, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 This is what the Lord, the God of Israel, says: I made a agreement with your forefathers when I led them out of Egypt, out of the prison-house of slavery, saying:
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
14 Every seventh year, each of you are to set free all fellow Hebrews who have sold themselves to you. They can serve you for six years, but then you must set them free. But your forefathers didn't pay attention and didn't obey what I told them.
‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
15 A little while ago you decided to do what's right, which made me happy. You all announced that you would free your slaves. You made a agreement before me in my Temple.
Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
16 But now you've changed your minds and dishonored me. Each of you took back the male and female slaves you'd set free to do whatever they wanted. You forced them to become your slaves again.
Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
17 So this is what the Lord says: You haven't obeyed me. You haven't announced freedom for your slaves, your own people. So now I announce “freedom” for you, declares the Lord: Freedom to be killed by war, by disease, and by famine! I will make all the kingdoms of the world horrified by you.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
18 They have broken my agreement, and have not kept the terms of the agreement they promised before me. So I'm going to cut them up just like the calf they cut in half to pass between its two pieces.
Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
19 I will hand them over to their enemies who are trying to kill them. This includes the leaders of Judah and Jerusalem, the court officials, the priests, and everyone else who passed between the pieces of the calf.
Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
20 Their dead bodies will become food for birds of prey and wild animals.
zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
21 I will hand over Zedekiah king of Judah and his officials to their enemies who are trying to kill them, to the army of the king of Babylon which had paused its attack on you.
“Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
22 Listen! I will give the order, declares the Lord, and bring them back to Jerusalem. They will attack it, capture it, and burn it. I'm going to destroy the towns of Judah so nobody will live there.
Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”

< Jeremiah 34 >