< Jeremiah 16 >
1 A message from the Lord that came to me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Don't marry or have children here.
“Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
3 This is what the Lord says about children born here, and about their mothers and fathers—their parents here in this country:
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
4 They will die from fatal diseases. No one will mourn for them. Their bodies won't be buried, but will lie on the ground like manure. They will be destroyed by war and famine, and their bodies will be food for birds of prey and wild animals.
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
5 This is what the Lord says: Don't enter a home where people are having a funeral meal. Don't visit them to mourn or to offer condolences, for I have taken away my peace, my trustworthy love, and my mercy from these people, declares the Lord.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
6 Everyone, from the most important to the least, will die in this country. They will not be buried or mourned; there will be no rites for the dead such as cutting oneself or shaving of heads.
“Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
7 No funeral receptions will be held to comfort those who mourn—not even a comforting drink is to be offered at the loss of a father or mother.
Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
8 Don't go into a house where people are celebrating and sit down with them to eat and drink.
“Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
9 This is what the Lord Almighty, the God of Israel, says: I am going to put a stop right here, while you watch, to any sounds of celebration and joy, the happy voices of the groom and bride.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
10 When you explain all this to them they'll ask you, “Why has the Lord ordered that such a terrible disaster should happen to us? What did we do wrong? What sin have we committed against the Lord our God?”
“Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
11 Answer them: It's because your forefathers deserted me, declares the Lord. They went and followed other gods, serving them and worshiping them. They abandoned me and didn't keep my laws.
Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
12 You however have done even more evil than your forefathers. Look at how all of you followed your own stubborn evil thinking instead of obeying me.
Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
13 So I'm going to throw you out of this country and exile you in a country unfamiliar to you and your forefathers. There you'll serve other gods day and night, because I won't help you at all.
Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
14 But listen! The time is coming, declares the Lord, when people won't any longer make vows, saying. “On the Lord's life, who led the Israelites out of Egypt.”
“Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
15 Instead they'll say, “On the Lord's life, who led the Israelites back from the northern country and all the other countries where he had exiled them.” I'm going to bring them back to the country I gave their forefathers.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
16 But for the moment I'm going to send for many fishermen and they'll catch them, declares the Lord. Then I'm going to send for many hunters, and they'll hunt them down on every mountain and hill, even from their hiding places in the rocks.
“Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
17 I see everything they're doing. They can't hide from me, and their sins aren't hidden from me either.
Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
18 First I'm going to pay them back double for their wickedness and sin, because they have made my land unclean with the lifeless bodies of their disgusting idols, filling my special country with their offensive pagan images.
Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
19 Lord, you are my strength and my fortress, my safe place in the time of trouble. Nations will come to you from all over the earth, and they will say, “The religion of our forefathers was a total lie! The idols they worshiped were useless—no good at all.
Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
20 How can people make gods for themselves? These aren't gods!”
Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
21 Now they'll see! I'll show them, and then they'll recognize my power and strength. Then they'll know that I am the Lord!
“Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.