< Isaiah 8 >

1 Then the Lord told me, “Get a large tablet and write on it in with an ordinary pen, ‘Maher-shalal-hash-baz.’
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 I will need Uriah the priest and Zechariah, son of Jeberekiah, to be my trustworthy witnesses.”
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Then I slept with my wife the prophetess, and she became pregnant and gave birth to a son. The Lord told me, “Call him Maher-shalal-hash-baz.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 For even before the boy knows how to say ‘Daddy’ or ‘Mommy,’ the king of Assyria will carry off Damascus' wealth and Samaria's possessions.”
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Then the Lord spoke to me again, saying,
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 “Because this people has rejected the waters of Shiloah that gently flow and instead have rejoiced with Rezin and Remaliah's son,
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 the Lord is going to bring the powerful floodwaters of the Euphrates River against them—the king of Assyria with all his glorious army. It will flood all its channels and overflow all its banks.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 It will sweep on into Judah, overflowing and flooding through, reaching up to the neck. Like outspread wings it will engulf the whole of your land, Immanuel!
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Pay attention, you nations, and be smashed! Listen, all you distant lands, get ready, but you will be smashed. Get ready, but you will be smashed.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 You can plan your strategy, but it will be foiled; you can say what you're intending, but it won't happen, for God is with us.”
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 For this is what the Lord told me, holding me with a strong hand, instructing me not to follow the way of this people. He said,
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Don't call a conspiracy everything that these people call a conspiracy. Don't fear what they fear. Don't be overawed!
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 The Lord Almighty is the one you should see as holy. He is the one you should fear, he is the one you should be in awe of.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 He will be a sanctuary for you. But to the royal families of both Israel and Judah he will be a stone they trip over and a rock that makes them stumble, a trap and a snare to the people who live in Jerusalem.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Many people will stumble over them. They will fall and be broken. They will be trapped and caught.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Safeguard this testimony, seal these instructions—they are for my disciples.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 I will wait for the Lord, the one who is hiding his face from Jacob's descendants. I will wait in hope for him.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Look, I'm here, together with the children the Lord has given me. They are signs and wonders in Israel from the Lord Almighty, who lives on Mount Zion.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 When someone suggests to you, “Go and ask mediums and spiritists who whisper and mutter,” shouldn't people ask their God? Why should they ask the dead on behalf of the living?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 Go and examine God's law and his instructions! If what they say doesn't correspond with God's word, there will be no dawn for them.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 They will wander round the country, depressed and hungry. When they are starving they will become furious, and looking up they will curse their king and their God.
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 Then they will look towards the earth and see only misery and gloom and agonizing depression, and they will be thrown out into the darkness.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.

< Isaiah 8 >