< Isaiah 64 >

1 If only you would rip the heavens apart and come down! The mountains would tremble in your presence!
Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
2 In the same way that fire burns wood and makes the water boil, make your reputation known to your enemies, so that nations will tremble in your presence!
Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
3 In the past you did things we weren't anticipating. You came down and the mountains trembled in your presence!
Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
4 Since the beginning, no one has heard about, no one has paid attention to, and no one has seen any God except you, the one who helps those who place their confidence in you.
Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
5 You join with those who are glad, and with those who do what's right and remember to follow your ways. But when we went on sinning, you became angry. How can we be saved if we go on like this?
Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
6 We've all become unclean, and all the good things we do are like dirty rags. We wither and die like autumn leaves, and our sins, like the wind, blow us away.
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
7 There's no one who calls for you or really wants to hold onto you, because you have hidden your face from us and let us drown in our own sins.
Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
8 But you, Lord, are our Father. We're the clay, you're the potter. You made us all with your own hands.
Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
9 Please limit your anger, Lord, and don't remember our sins forever. Look at us, and see that we are all your people.
Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
10 Your holy cities have been turned into a wilderness; Zion has become a desert; yes, even Jerusalem is an abandoned ruin.
Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
11 Our beautiful, holy Temple where our forefathers praised you has been burned down, and all that we treasured has been destroyed.
Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
12 In view of all this, are you still going to refuse to help us? Are you going to stay quiet and punish us so severely?
Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?

< Isaiah 64 >