< Isaiah 49 >
1 Listen to me, you people of the islands! Pay attention, you who live far away! The Lord called me before I was born; he gave me my name while I was still in my mother's womb.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 The words he gave me to speak are like a sharp sword. He has protected me by covering me with his hand. He put me in his quiver like a sharp arrow, keeping me safe there.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 He told me, “You are my servant, Israel, and I will reveal my glory through you.”
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 But I replied, “I've worked for nothing! I've exhausted myself, and for what? Even so, I leave it with the Lord to do what's right, and my reward is with my God.”
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Now my Lord is going to speak, the one who formed me in the womb as his servant to bring Jacob back to him, to gather Israel to himself. I am honored in the Lord's sight, and my God has given me strength.
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 He says, “It's nothing much for you to be my servant to bring back the tribes of Jacob, those people of Israel that I've preserved. I'm also going to make you a light for the foreigners so that my salvation may reach everybody.”
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 This is what the Lord says, the Redeemer and Holy One of Israel, to the one who was despised and detested by the nation, to the one who is the servant of rulers: Kings will see you and stand up, and princes will bow down to you, because the Lord, who is trustworthy, the Holy One of Israel, has chosen you.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 This is what the Lord says: I will answer you at the proper time; I will help you on the day of salvation. I will take care of you, and I will give you to the people as my agreement with them, to restore the land and to reassign the parts that have been abandoned.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 Tell the prisoners, “Come out!” Tell those living in darkness, “Come into the light!” Like sheep they will feed along the roads and in the pastures on hills that once were barren.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 They won't be hungry or thirsty, and they won't get hot in the sun, for the one who loves them will lead them to springs, and guide them to water.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 I will turn all my mountains into a road; my highways will be really high!
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Look at these people coming from far away! Look at these people coming from the north, and from the west, and from Upper Egypt.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Heavens, shout for joy! Earth, celebrate! Mountains, sing out in happiness! The Lord has come to care for his people, and he will treat his suffering people kindly.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 But Zion said, “The Lord has given up on me; the Lord has forgotten about me.”
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Really? Can a mother forget her nursing baby? Can she forget to be kind to the child she carried in her womb? Even if she could forget, I will never forget you!
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Look at your names I've written on the palms of my hands! I'm always thinking about your walls.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Soon your children will come running back. Your destroyers, those that devastated your land, will be gone.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Take a look around. See all your children gathering and coming back to you. As I live, declares the Lord, you will wear them all as jewelry, proudly putting them on like a bride.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Your ruined towns and abandoned places and devastated lands will be crowded with people, while those who took over your country will be long gone.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 The children born during your time of mourning in exile will say, “This place is too crowded for me! Make room so I have a place to live!”
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Then you will say to yourself, “Who gave birth to all these children for me? My children were killed and I was unable to have more; I was exiled and thrown aside—so who brought these children up? Look, I was abandoned, so where did they come from?”
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 This is what the Lord God says, Watch as I give the signal to the nations, as I raise my flag to let everyone know. They will bring them back, carrying your sons in their arms, and lifting your daughters onto their shoulders.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Kings will be your child-minders; queens will be your nurses. They will bow low before you, and lick the dust from your feet. Then you will know that I am the Lord, and that those who put their trust in me will never be ashamed.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Can loot be taken from a warrior? Can prisoners be rescued from a dictator?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 But this is what the Lord says: Even the prisoners of warriors will be won back; even loot will be recovered from a dictator. I will fight with your enemies, and I will rescue your children.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 I will make your oppressors eat their own flesh and drink their own blood like wine. Then everyone will know that I, the Lord, am your Savior and Redeemer, the Mighty One of Israel.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”