< Isaiah 24 >
1 Watch out! The Lord is going to destroy the earth, to make it totally devastated. He's going to rip up the surface of the earth and scatter its inhabitants.
Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
2 It will happen the same for everybody—whether people or priests, servants or their masters, maids or their mistresses, buyers or sellers, lenders or borrowers, creditors or debtors.
zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
3 The earth will be completely laid waste and looted. This is what the Lord has said.
Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
4 The earth dries up and withers away; the world shrivels up and withers away, the high and mighty people shrivel up along with the earth.
Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
5 The earth is polluted by its people; they have flouted God's laws, violated his regulations, and broken the eternal agreement with him.
Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
6 That is why a curse is destroying the earth. The people suffer because of their guilt. The inhabitants of the earth are burned up and only a few survive.
Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
7 The new wine dries up, and the vine withers. All the people celebrating groan.
Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
8 The happy sound of tambourines is over; the noise of the party-goers has stopped; the delightful harp music has finished,
Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
9 People don't sing any more as they drink wine, and the beer tastes bitter.
Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
10 The chaotic city is falling apart; every house is barred shut to keep others out.
Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
11 Crowds on the street are shouting, demanding to have wine. Joy turns into darkness. There's no happiness left on earth.
A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
12 The city is in a horrible state of ruin; its gates have been broken down.
An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
13 This is the way it's going to be all throughout the earth among the nations—only a few olives are left after the tree is shaken, only a few grapes are left to be gleaned after the harvest.
Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
14 These survivors shout aloud and sing for joy. From the west they praise the Lord's majesty.
Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
15 From the east they glorify the Lord; from the sea shores they praise the name of the Lord, the God of Israel.
Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
16 We hear songs coming from the ends of the earth, singing, “Glory to the God who does right.” But I'm miserable, miserable. Pity me! Deceitful people go on betraying, again and again.
Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
17 Terrors and pit-traps and snares are waiting for you, people of the earth.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
18 Those who run away in terror will fall into a pit-trap, and those who escape from the pit-trap will be caught in a snare. Heaven's windows are opened; earth's foundations shake.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
19 The earth is completely broken up; the earth is ripped apart, the earth is violently shaken.
An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
20 The earth staggers to and fro like a drunk, and sways this way and that like a shelter. The guilt of its rebelliousness weighs heavily on it, and it collapses—it won't rise again.
Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
21 At that time the Lord will punish all the high heavenly beings and the kings of the earth.
A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
22 They will be brought together, prisoners in a pit. They will be imprisoned, and eventually they will be punished.
Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
23 The moon will be embarrassed and the sun will be ashamed, for the Lord Almighty will reign in glory on Mount Zion and in Jerusalem in the presence of its leaders.
Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.