< Hosea 4 >

1 Hear the word of the Lord, people of Israel, for the Lord has an accusation against the inhabitants of the land! “There is no faithfulness, no loyalty, and no knowledge of God in the land.
Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
2 Instead there is only cursing, lying, murdering, stealing, and adultery. They commit violence, and bloodshed follows bloodshed.
Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
3 As a result the land dries up, and everyone who lives there is wasting away, along with the wild animals and the birds of the sky and the fish of the sea—they are all dying.
Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
4 But no one should accuse or blame anyone else. My quarrel is with you the priests—you are the ones responsible.
“Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
5 Consequently you will stumble in daylight, and the prophet will stumble together with you in the night, and I will destroy your mother.
Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
6 My people are dying because they don't know me. Because you have refused to know me, I refuse to accept you as my priests. You have forgotten my teachings, so I will forget your children.
mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
7 The more there were of them, the more they sinned against me, so I will change their glory into shame.
Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
8 They feed on the sin of my people, greedy for their iniquity.
Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
9 So it will be for the people like the priests: I will punish them for what they have done, repaying them for their actions.
Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
10 They will eat, but they will not be satisfied; they will engage in prostitution, but they will not prosper because they have given up on the Lord to go and prostitute themselves to other gods.
“Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
11 They destroy their minds with old wine and new wine.
ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
12 My people consult their wooden idols and their divining rods give them answers, for a spirit of prostitution makes them go astray. Prostituting themselves, they have deserted their God.
Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
13 They offer sacrifices on the tops of mountains; they burn incense in the hills under the oak, poplar, and terebinth trees where the shade is pleasant. That's the reason why your daughters practice prostitution and your daughters-in-law commit adultery.
Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
14 I will not punish your daughters when they practice prostitution, nor your daughters-in-law when they commit adultery, because you men visit whores and sacrifice with temple prostitutes. A people who lack understanding end up in disaster.
“Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
15 Though you, Israel, have become a prostitute, may Judah not offend in the same way and not enter Gilgal, nor go up to Beth-aven, nor swear saying, ‘the Lord lives.’
“Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
16 For Israel is as stubborn as a stubborn cow. Should the Lord then take care of them like a lamb in a wide pasture?
Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
17 Ephraim is bewitched by idols, so leave him alone!
Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
18 Once the leaders finish drinking, they go off and find prostitutes to sleep with. They love their shameful acts more than honor.
Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
19 A wind will carry them away; they will be ashamed of their pagan worship.
Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.

< Hosea 4 >