< Hosea 1 >
1 The Lord sent a message to Hosea son of Beeri at the time when Uzziah, Jotham, and Ahaz were the kings of Judah, and Jeroboam son of Jehoash was the king of Israel.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 The Lord began speaking through Hosea by telling him, “Go and take a wife who is a prostitute and have children born to a prostitute because those living in this land have committed terrible prostitution by turning away from the Lord.”
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 So Hosea went and married Gomer, the daughter of Diblaim. She became pregnant and bore Hosea a son.
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 The Lord told Hosea, “Call him Jezreel, because I am going to punish the house of Jehu for the blood he shed at Jezreel, and I will put an end to the kingdom of Israel.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 On that day I will break Israel's military power in the valley of Jezreel.”
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 Gomer became pregnant again and gave birth to a daughter. The Lord told Hosea, “Call her Lo-ruhamah, because I will no longer love the house of Israel and certainly not forgive them.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 But I will have pity on the house of Judah, and I will save them—but I will not save them by bow or sword or war or horses and riders.”
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 After Gomer had weaned Lo-ruhamah she became pregnant again and gave birth to a son.
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 The Lord told Hosea, “Call him Lo-ammi, because you are not my people and I am not your God.
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 Even so the number of the people of Israel will be like the sand on the seashore that cannot be measured or counted. Then right there at the place where they were told ‘you are not my people’ they will be called ‘the children of the living God.’
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 The people of Israel and the people of Judah will be gathered together and they will choose one leader for themselves and they will take possession of the land, and the day of Jezreel will be great.”
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.