< Genesis 11 >
1 At that time the whole world spoke just one language and used words with the same meaning.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 As they moved east they discovered a plain in the land of Shinar so they settled there.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 They said to one another, “Come on, let's make some bricks and bake them with fire.” (They used brick instead of stone, and tar instead of cement).
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 Then they said, “Now let's build a city for ourselves with a tower whose top reaches the heavens. That way we'll gain a great reputation and we won't end up being scattered all over the world.”
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 But the Lord came down to take a look at the city and the tower that the people were building.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 The Lord said, “Look! These people are united and they all speak one language. If this is what they can do now when they're just getting started, nothing will be impossible for them when they all put their minds to it!
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 We need to go down and mix up their language and make it confused so they won't be able to understand what they're saying to one other.”
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 The Lord sent them away from there and scattered them all over the world, and they gave up building the city.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 That's why it was called Babel, because the Lord made the language of the world confused.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 The following is the genealogy of Shem. When Shem was 100, he had Arphaxad. This was two years after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 Shem lived another 500 years after Arphaxad was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 When Arphaxad was 35, he had Shelah.
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 Arphaxad lived another 403 years after Shelah was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 When Shelah was 30, he had Eber.
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 Shelah lived another 403 years after Eber was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 When Eber was 34, he had Peleg.
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 Eber lived another 430 years after Peleg was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 When Peleg was 30, he had Reu.
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 Peleg lived another 209 years after Reu was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 When Reu was 32, he had Serug.
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 Reu lived another 207 years after Serug was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 When Serug was 30, he had Nahor.
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 Serug lived another 200 years after Nahor was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 When Nahor was 29, he had Terah.
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 Nahor lived another 119 years after Terah was born and had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 When Terah was 70, he had Abram, Nahor, and Haran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 The following is the genealogy of Terah. Terah was the father of Abram, Nahor, and Haran. Haran was the father of Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 However, Haran died while his father, Terah, was still alive, in Ur of the Chaldeans, the land of his birth.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 Abram and Nahor both got married. Abram's wife was named Sarai, and Nahor's wife was named Milcah. (She was the daughter of Haran, who was the father of both Milcah and Iscah).
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 Sarai wasn't able to become pregnant and so had no children.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 Terah took his son Abram, his grandson Lot, (who was the son of Haran), his daughter-in-law Sarai, (the wife of his son Abram), and left Ur of the Chaldeans to move to the land of Canaan. They got as far as Haran and settled there.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 Terah lived for 205 years and died in Haran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.