< Ezekiel 4 >

1 “Son of man, you are to take a brick, put in front of you, and draw a picture of the city of Jerusalem on it.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
2 Show that it's under siege: establish a siege perimeter all around it, build a siege ramp against it, set up the enemy camps beside it, and put battering rams on all sides around it.
Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
3 Put an iron plate between yourself and the city so it's like an iron wall. Face the city and demonstrate that it's under siege, and that you are the one attacking it. This is a symbolic warning to the people of Israel.
Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
4 Then lie on your left side and take the Israelites' sins on yourself. You will carry their sins for the number of days you lie on your side.
“Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
5 I will make you stay there for 390 days, representing the number of years of their sins. You will bear the sins of the Israelites.
Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
6 Once you have finished doing this for these days, then you are to lie down again, but this time on your right side, and carry the sins of the people of Judah. I will make you stay there for 40 days, one day for every year.
“Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
7 Keep your face towards the siege of Jerusalem with your arm bared, and prophesy against it.
Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
8 Be ready, because now I'm going to tie you up with ropes so you can't move from side to side until the days of your siege are over.
Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
9 Get some wheat, barley, beans, lentils, millet, and spelt, and mix them together in a storage jar. Use them to make bread for yourself. This is what you are to eat for the 390 days that you lie on your side.
“Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
10 You are allowed to eat twenty shekels weight of food each day, and you are to eat it at regular times.
Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
11 Measure out a sixth of a hin of water to drink, and you are to drink it at regular times.
Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
12 You are to eat the bread as you would a barley loaf. You are to bake it over a fire burning dried human excrement as everyone watches.”
Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
13 Then the Lord said, “This is the way the Israelites will eat their unclean bread among the nations where I'll exile them.”
Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
14 “Please no, Lord God!” I answered. “I have never made myself unclean. I haven't eaten anything found dead or killed by wild animals from the time I was young until now. I've never put unclean meat in my mouth.”
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
15 “All right,” he said. “I'll let you use cow manure instead of human excrement You can bake your bread over a fire using that.”
Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
16 Then he went on, “Son of man, watch! I am going to put a stop to Jerusalem's food supply. Worried sick, they will eat bread rationed by weight. Despairing at what's happening, they will drink water measured in small amounts.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
17 Running out of food and water, they will be horrified as they look at one another wasting away because of their sins.”
domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.

< Ezekiel 4 >